Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu
Published: March 19, 2026 at 8:54 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Masoya kungiyar kwallan kafa ta kasar Morocco sun nuna farin ciki bisa hukuncin da kotu ta yanke na baiwa kungiyar nasarar cin gasan kwallon kofi na nahiyar Afirka da ci 3-0 kan kasar Senegal. Amma wasu sun ce a bi abun a sannu, yayin da Senegal ke shirin daukaka kara don kalubalantar hukuncin da ya girgiza harkar kwallon kafa a nahiyar afirka.

Hukumar kwallon kafa ta Afirka wato (CAF) ta ayyana kasar Morocco a matsayin wadda ta lashe gasar, bayan da tayi hukuncin cewa ‘yan wasan Senegal sun rasa damar su bayan da suka fice daga fili na tsawon mintuna 14 don nuna adawa da penalty da aka bawa daya bangaren.

Duk da Senegal ta dawo daga baya ta kuma ci kwallo daya a karin lokaci da aka bayar, yayin da Morocco bata ci komai ba, CAF ta sauya sakamakon, inda ta bawa Morocco ci 3, ita kuma Senegal ba ko daya.

Hukumar kwallon kafa ta Senegal tace zata daukaka kara kan wannan hukunci da ba’a taba ganin irin sa ba, kuma baza’a yadda dashi ba. Ita kuma kungiyar kwallon kafa ta Morocco tace daukan tsauraran matakai zai taimakawa kwallon kafa a Afirka.

Afrika, Labarai, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas
Next Post: Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu Afrika
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.