Iran ta kai hari kan wata matatar mai a Kuwait ranar jumma’a, Isra’ila kuma ta kashe kakakin rundunar juyin juya hali na Iran, yayinda ake ganin wannan yaki na hadin guiwar Amurka da Isra’ila kan Iran bai nuna wata alamar kawo karshe ba.
Isra’ila tayi alkawarin ba zata sake kai hari kan cibiyar iskar gas na Iran da ake kira ko yake kudancin Pars, wadda Iran ta dauki fansa kan Qatar, da yayi mummmunar ta’adi da aka ce zai janyo wa duniya karancin iskar Gas da zai dauki shekaru masu yawa.
Yayinda Musulmi a yankin kamar sauran Musulmi suke kokarin sallar idi, na kammala watan azumi, a kuma dai dai da bikin Nowuz, watau sabuwar shekara ga Farisawa, zaton kawo karshen yakin da yake shiga mako na hudu, zuwa yanzu dai ba’a ga alama ba.
Farashin mai da ake kira Brent ya sassauto kadan zuwa dala 108 kan ko wace ganga, bayan da yayi tashin gwaron zabbi ranar Alhamis, saboda faragabar duk cikas da aka samu wajen wadatar makamashi zai yi illa ga tattalin arzikin duniya.
Koda an tsaida yakin nan bada jumawa ba, ba za’a sami waraka cikin gaggawa ba sakamakon fitintinun da suka biyo bayan farmaki daga sama, da kuma rufe mashigin ruwan Hormuz da Iran tayi, wacce itace hanyar da ake bi domin jigilar kashi 20 cikin dari na mai da iskar gas da duniya take amfani dashi.
Kasashen Jamus, da Britaniya, da Faransa, da Italiya, da Netherlands, da japan, ranar Alhamis, a wata sanarwa ta hadin gwiwa da suka fitar, sunyi alkawarin daukar matakai da suka wajaba na tabbtar da ganin zirga zirga ta tabbata a mshigin ruwan Hormuz, amma wazirin Jamus ko Chancellor Friedrich Merz, yace hakan zai ta’allaka ne idan aka kawo karshen yakin.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron, bayan taron koli na kungiyar tarayyar turai tayi a Brussels, yace kare dokokin kasa da kasa, da kuma sassauta rikici shine “gwargwadon abunda zamu iya yi,” ya kara da cewa ban ji wani anan wanda ya bayyana sha’awar shiga wannan rikici ba.
Shugaban Amurka Donald Trump, a ranar jumma’a, ya kira kawayen Amurka da suke cikin Kungiyar tsaro ta NATO, a zaman ragaye, saboda sunki su taimaka a yakin Iran, da suka hada da kasa daukar mataki mafi sauki na tabbatar da mashigin ruwan Hormuz yana bude, amma suna da bakin kukan cewa mai yayi tsada.
Ahalinda ake ciki kuma, Amurka zata tura karin dubban sojojinta na kundun bala zuwa gabas ta tsakiya, kamar yadda wasu majiyoyi uku da suke da masanaiya kan lamarin suka shaidawa kamfanin dilancin labarai na Reuters a ranar Jumma’a. A kuma dai dai lokacin da sabon shugaban addinin Iran ya yaba da hadin kan kasar, da kuma “turjiyar da suke nunawa.”


