Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait
Published: March 20, 2026 at 9:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Iran ta kai hari kan wata matatar mai a Kuwait ranar jumma’a, Isra’ila kuma ta kashe kakakin rundunar juyin juya hali na Iran, yayinda ake ganin wannan yaki na hadin guiwar Amurka da Isra’ila kan Iran bai nuna wata alamar kawo karshe ba.

Isra’ila tayi alkawarin ba zata sake kai hari kan cibiyar iskar gas na Iran da ake kira ko yake kudancin Pars, wadda Iran ta dauki fansa kan Qatar, da yayi mummmunar ta’adi da aka ce zai janyo wa duniya karancin iskar Gas da zai dauki shekaru masu yawa.

Yayinda Musulmi a yankin kamar sauran Musulmi suke kokarin sallar idi, na kammala watan azumi, a kuma dai dai da bikin Nowuz, watau sabuwar shekara ga Farisawa, zaton kawo karshen yakin da yake shiga mako na hudu, zuwa yanzu dai ba’a ga alama ba.

Farashin mai da ake kira Brent ya sassauto kadan zuwa dala 108 kan ko wace ganga, bayan da yayi tashin gwaron zabbi ranar Alhamis, saboda faragabar duk cikas da aka samu wajen wadatar makamashi zai yi illa ga tattalin arzikin duniya.

Koda an tsaida yakin nan bada jumawa ba, ba za’a sami waraka cikin gaggawa ba sakamakon fitintinun da suka biyo bayan farmaki daga sama, da kuma rufe mashigin ruwan Hormuz da Iran tayi, wacce itace hanyar da ake bi domin jigilar kashi 20 cikin dari na mai da iskar gas da duniya take amfani dashi.

Kasashen Jamus, da Britaniya, da Faransa, da Italiya, da Netherlands, da japan, ranar Alhamis, a wata sanarwa ta hadin gwiwa da suka fitar, sunyi alkawarin daukar matakai da suka wajaba na tabbtar da ganin zirga zirga ta tabbata a mshigin ruwan Hormuz, amma wazirin Jamus ko Chancellor Friedrich Merz, yace hakan zai ta’allaka ne idan aka kawo karshen yakin.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron, bayan taron koli na kungiyar tarayyar turai tayi a Brussels, yace kare dokokin kasa da kasa, da kuma sassauta rikici shine “gwargwadon abunda zamu iya yi,” ya kara da cewa ban ji wani anan wanda ya bayyana sha’awar shiga wannan rikici ba.

Shugaban Amurka Donald Trump, a ranar jumma’a, ya kira kawayen Amurka da suke cikin Kungiyar tsaro ta NATO, a zaman ragaye, saboda sunki su taimaka a yakin Iran, da suka hada da kasa daukar mataki mafi sauki na tabbatar da mashigin ruwan Hormuz yana bude, amma suna da bakin kukan cewa mai yayi tsada.

Ahalinda ake ciki kuma, Amurka zata tura karin dubban sojojinta na kundun bala zuwa gabas ta tsakiya, kamar yadda wasu majiyoyi uku da suke da masanaiya kan lamarin suka shaidawa kamfanin dilancin labarai na Reuters a ranar Jumma’a. A kuma dai dai lokacin da sabon shugaban addinin Iran ya yaba da hadin kan kasar, da kuma “turjiyar da suke nunawa.”

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros
Next Post: Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala Afrika
Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
  • ‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.