Rundunar mayakan Amurka zata tura karin dubban sojojin kundubalarta zuwa gabas ta tsakiya, kamar yadda wasu jami’ai suka fadawa kamfanin dillanciin labarai na Reuters jiya jumma’a, yayinda shugaban Amurka Donald Trump ya zargi kawayen Washinghton dake kungiyar tsaro ta NATO da cewa su ragaye ne saboda sun gaza tura dakarun su su taimakawa wajen bude mashigin ruwan Hormuz.
Mashigin ruwan, inda ta nan ne ake bi da kashi 20 cikin dari na mai da iskar gas da duniya take amfani dashi, kusan Iran ta rufe shi baki daya, tun lokacin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da yaki kan Iran kusan makonni uku da suka wuce.
Kadarorin mai a Iran da kuma kasashe makabtanta duk an kai musu hari, saboda haka farashin mai ya tashi da kusan kashi 50 cikin dari tun bayan fara yakin ranar 28 ga watan Febwairu, wanda hakan yake barazana ga tattalin arzikin duniya.
An kashe mutane fiye da dubu biyu-galibin su a Iran da kuma Lebanon, su kuma Amurkawa da suke fuskantar tsadar mai, suna kara nuna damuwa ganin alamun yakin zai fadada.
Wata kuri’ar neman jin ra’ayin jama’a da kamfanin dillancin labarai na Reuters da IPSOS suka gudanar, rabin Amurkawa sun hakikance cewa shugaba Trump zai tura sojojin kasa domin yakin, inda kashi 7 cikin dari ne kawai suke goyon bayan matakin haka.


