Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026
Published: November 26, 2025 at 3:23 PM | By: Nafisa Ahmad

Da alamun Cristioano Ronaldo zai buga ma Portugal dukkan wasanninta a gasar cin kofin kwallon kafar duniya ta shekara mai zuwa, duk da jan katin da aka ba shi lokacin da ya buge wani dan wasan Ireland da gwiwar hannu.

A yau Talata hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta wallafa hukumcin dakatar da shi daga wasanni uku da ta yanke, amma ta ce wasa daya dole zai rasa, sauran biyu kuma an dage hukumci a kansu har na tsawon shekara guda domin a ga ko zai sake aikata irin abinda yayi har aka ba shi jan katin.

An dakatar da Ronaldo daga buga wasa guda na tilas a lokacin da kasarsa ta buga da Armeniya ta lashe da ci 9-1, abinda ya tabbatar da gurbinta a gasar cin kofin duniyar da za a yi a nan yankin nahiyar Amurka ta arewa a shekara mai zuwa.

Masu fashin baki da dama sun dauka cewa za a dakatar da Ronaldo daga karin wasa guda, ta yadda za a fara buga gasar cin kofin duniyar ba tare da shi ba.

Wannan shine karo na 6 da Ronaldo zai buga ma Portugal kwallo a gasar cin kofin duniya, abinda babu wani dan wasan da ya taba haka.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL
Next Post: Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari

Karin Labarai Masu Alaka

Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba” Wasanni
Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni
Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
  • Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
  • Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.