Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Hukumar Tsaron Teku A Libya Tafara Janye Jirgi Mai Dauke Da Iskar Gas
Published: March 26, 2026 at 10:09 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar tsaron gabar tekun Libya ta fara jan wani jirgin ruwa mai ɗauke da iskar gas mai narkewa (LNG) da ya lalace, wanda ƙasashen yankin Bahar Rum da dama suka yi gargadin cewa na iya haifar da haɗarin muhalli, bayan ya yi makonni yana yawo ba tare da matuƙa ba, kamar yadda Gwamnatin Haɗin Kan Ƙasa da ke Tripoli (GNU) ta bayyana.

Jirgin mai ɗauke da tutar Rasha mai suna Arctic Metagaz, wanda ke ɗauke da iskar LNG daga tashar Murmansk ta yankin Arctic, ya kasance yana yawo tun farkon watan Maris, lokacin da Ma’aikatar Sufuri ta Rasha ta ce jiragen ruwa marasa matuƙa na Ukraine sun kai masa hari.

Ba tare da ma’aikata a cikinsa ba, daga ƙarshe jirgin ya kusanto gabar tashar jiragen ruwa ta Zuwara da ke yammacin Libya.

Ƙasashen Italy, France, Spain da wasu ƙasashe shida (6) na kudancin Tarayyar Turai sun aika wasiƙa ga Hukumar Tarayyar Turai a makon da ya gabata, suna gargadin cewa jirgin na haifar da “barazana ta gaggawa kuma mai tsanani ga wani babban bala’in muhalli.”

Ministan Sufuri na gwamnatin GNU, Mohamed Al-Shahoubi, ya ce a cikin wani saƙon bidiyo cewa an ɗora wa Hukumar Mai ta Ƙasa a Libya alhakin sauke kayan da ke cikin jirgin na Rasha. Ya ƙara da cewa ana haɗa kai ta hannun Ma’aikatar Harkokin Waje da hukumomin Rasha da Malta domin ɗaukar matakan tabbatar da tsaron zirga-zirgar ruwa a yankin Bahar Rum.

Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri
Next Post: Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai
Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
  • Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
  • Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.