Isra’ila ta cire sunan ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da kakakin majalisar kasar Mohammad Baqer Qalibaf daga jerin mutanen da suke fakon ran su bayan da Pakistan ta bukaci fadar Washington da ta matsawa Isra’ila kada ta nemi kashe su, kamar yadda wani dan Pakistan dake da masaniya kan abun ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters a jiya Alhamis.
Sojojin Pakistan da ofishin harkokin waje na kasar basu mai da martani kan tambayoyin da ya shafi abin ba.
Mujallar Wall Street ta ruwaito cewa an cire manyan jami’an na Iran su biyu na wucen gadi na kwanaki 4 zuwa 5 daga jerin mutanen da Isra’ila ke so kashewa, a lokacin da suke duba yuwuwar tattaunawar kawo zaman lafiya, a cewar mujallar a fadar jami’an Amurka, amma bata ambaci sa hannun Pakistan a ciki ba.


