Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana
Published: March 27, 2026 at 7:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Dinkin Duniya ta amince da kudurin da kasar Ghana ta gabatar a ranar Laraba na ta yarda da bautar da mutane a ketaren tekun Atlantika a matsayin laifi mafi muni ga dan Adam, kuma an yarda da kudurin neman diyya, duk da bijirewa da aka samu daga Turai da kuma Amurka.

Ghana tace ana bukatar wannan kuduri, saboda abunda bautar da mutane ya haddasa, inda aka dauki a kalla mutanen Afrika miliyan 12 da dubu 500, aka sayar da su tsakanin karni na 15 zuwa karni na 19, har yau ana fuskantar sa, ciki har da wariyar launin fata.

A kuri’ar da aka kada a babban taro na Majalisar Dinkin Duniya, kasashe 123 sun goyi bayan kudurin, uku kuma basu goyi baya ba, cikin su akwai Amurka da Isra’ila, sannan kasashe 52 basu kada kuri’a ba, ciki da Tarayya Turai da Birtaniya.

Justin Howard, Ferfesa a Fannin Shari’a a jami’ar Howard yace kudurin nada muhimmanci, saboda yana nuni da matakin koli da Majalisar Dinkin Duniya ta dauka wajen amincewa da bautar da mutane a ketaren tekun Atlantika a matsayin cin zarafin dan adam, da kuma kira da a biya diyya.

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya shaidawa babban taron Majalisar cewa ana bukatar sauran kasashe su dauki mataki don fuskantar rashin adalcin da aka tafka a baya. Kasar Netherlands har yanzu ita ce kasa daya tilo a Turai da ta bayar da hakuri kan rawar da ta taka a bautar da mutane.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako
Next Post: Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
  • Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika
  • Majalisa A Kasar Somaliya Ta Amince Da Sauya Tsarin Mulkin Kasar Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.