Magungunan cutar kolera da aka tanadar domin kasashen Afirka da dama sun makale a dubai sakamakon yakin hadin guiwar da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran, lamari da yake kara janyo Fargaba kan shirye shiryen da ake yi ganin damuna ta karato na tunkarar cutar da take saurin yaduwa da take haddasa gudawa, kamar yadda ma’aikatan kiwon lafiya suka gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Kayayyakin jinyar da aka tanadar musamman ga yankunan da aka saba fuskantar cutar da suka hada da Chadi, da Sudan, gabannin damina da galibi take kankama cikin watan Mayu, da nufin shawo kan cutar kamin ta bazu.
Hukumar kiwon lafiya ta duniya da ake kira WHO a takaice, da kuma kungiyoyin agaji na Red Cross da Red Crescent, duk sun gayawa kamfanin diillancin labarai na Reuters cewa, kodai suyi jigilar magungunan da jiragen sama wanda zai kara kudin jigilar da kamar kashi 70 cikin dari, ko kuma sayi wasu daban.


