A yanzu adadin mutanen da suka rasa rayukan su sakamakon ambaliyar ruwa a kasar Kenya ya kai 108, a cewar ‘yan sanda ranar Asabar.
Ambaliyar ruwa da ya fara ranar 6 ga Watan Maris, ya jawo barna da dama a Kenya, inda ya tafi da gomman motoci, ya kawo tsaiko ga zirga-zirgar jiragen sama, ya kuma bata wayoyin lantarki na kasar.
Fiye da magidanta 2700 suka rasa matsugunin su a fadin kasar, a cewar hukumomi a ranar Jumu’a.
Duk da cewa tsananin ruwan sama ya lafa, ‘yan sanda sun yi gargadin cewa har yanzu akwai hadarin ambaliyar ruwa saboda cika da batsewa da magudanan ruwa suka yi.


