Ministan tsaron Isra’ila ya fada ranar talata cewa, Isra’ila zata rusa dukkan gidaje da suke kauyuka da suke kan iyakarta da Lebanon, kuma mutane dubu dari shida da suka gudu daga muhallan su ba zata kale su koma gidajen su ba, har sai bani yahudun taga arewacin kasar ya sammu tsaro, yana mai alwashin cewa zata ragagarza yankin na Lebanon shigen irin abunda ta aiwatar a Gaza.
Isra’ila Katz ya sake nanata kudurin hukumomi da suke Tel-Aviv na kirkiro yankin da ta kira na tsaro a kudancin Lebanon daga kan iyakarta har zuwa kogin da ake kira Litani, da zarar ta kammala yaki da Iran.
Mutane fiye da milyan daya da dubu dari hudu ne suka rasa muhallan su a Lebanon, yayinda wasu dubu daya da dari biyu suka halaka, tun lokacin da Isra’ila ta kaddamar da hari kan kasar ranar biyu ga watan nan na Maris, sakamakon hari da Kungiyar Hesbollah ta auna kan kasar, zaman martani ko goyon bayan Iran a yaki da take yi da Amurka da Isra’ila.


