Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos
Published: April 2, 2026 at 1:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, a ranar Alhamis 2 ga Afrilu, 2026, ya jagoranci shugabannin hukumomin tsaro domin duba halin tsaro kai tsaye a birnin Jos na jihar Filato

Mukaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji, Kanal Appolonia Anele, ta bayyana a wata sanarwa cewa ziyarar na daga cikin ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da tabbatar da dorewar sa a faɗin jihar.

Sanarwar ta ce, bayan isowarsa ya samu tarba daga gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, a matsayin alamar kyakkyawar haɗin gwiwa tsakanin farar hula da sojoji wajen magance matsalolin tsaro.

Haka kuma, COAS ya karɓi cikakken bayani kan ayyukan tsaro daga Babban Kwamandan Runduna ta 3 da kuma Kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta Operation ENDURING PEACE, Manjo Janar Folusho Oyinlola, wanda ya yi bayani kan matakan da ake ɗauka tare da sauran hukumomin tsaro domin dakile barazana, kare rayuka da dukiyoyi, da kuma daidaita al’ummomin da abin ya shafa.

A yayin ziyarar, Laftanar Janar Waidi Shaibu ya gana da shugabannin al’umma da mazauna yankin, inda ya tabbatar musu da ƙudirin rundunar sojin kasa ta Najeriya na kare rayukan dukkan ‘yan ƙasa masu bin doka.

Ya kuma buƙaci al’umma su kasance cikin natsuwa da taka-tsantsan, su kuma mara wa hukumomin tsaro baya ta hanyar bin dokar takaita zirga-zirga (curfew) da kuma ba da cikakken haɗin kai a ayyukan bincike da tsaro, yayin da suke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Shugaban ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, Mr. Dachung Bagos, ya yaba da ziyarar COAS, yana mai cewa zuwan manyan shugabannin soji zai ƙara wa jama’a kwarin gwiwa tare da ƙarfafa amincewa da matakan tsaro da ake ɗauka.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi
Next Post: Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan

Karin Labarai Masu Alaka

NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
NDPHC Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Gombe Wajen Inganta Wutar Lantarki Afrika
Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
Shari’ar Ta’addanci: Manyan Jagororin Ansaru Biyu Sun Amsa Laifi A Abuja Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi Labarai
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.