Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos
Published: April 2, 2026 at 1:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, a ranar Alhamis 2 ga Afrilu, 2026, ya jagoranci shugabannin hukumomin tsaro domin duba halin tsaro kai tsaye a birnin Jos na jihar Filato

Mukaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji, Kanal Appolonia Anele, ta bayyana a wata sanarwa cewa ziyarar na daga cikin ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da tabbatar da dorewar sa a faɗin jihar.

Sanarwar ta ce, bayan isowarsa ya samu tarba daga gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, a matsayin alamar kyakkyawar haɗin gwiwa tsakanin farar hula da sojoji wajen magance matsalolin tsaro.

Haka kuma, COAS ya karɓi cikakken bayani kan ayyukan tsaro daga Babban Kwamandan Runduna ta 3 da kuma Kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta Operation ENDURING PEACE, Manjo Janar Folusho Oyinlola, wanda ya yi bayani kan matakan da ake ɗauka tare da sauran hukumomin tsaro domin dakile barazana, kare rayuka da dukiyoyi, da kuma daidaita al’ummomin da abin ya shafa.

A yayin ziyarar, Laftanar Janar Waidi Shaibu ya gana da shugabannin al’umma da mazauna yankin, inda ya tabbatar musu da ƙudirin rundunar sojin kasa ta Najeriya na kare rayukan dukkan ‘yan ƙasa masu bin doka.

Ya kuma buƙaci al’umma su kasance cikin natsuwa da taka-tsantsan, su kuma mara wa hukumomin tsaro baya ta hanyar bin dokar takaita zirga-zirga (curfew) da kuma ba da cikakken haɗin kai a ayyukan bincike da tsaro, yayin da suke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Shugaban ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, Mr. Dachung Bagos, ya yaba da ziyarar COAS, yana mai cewa zuwan manyan shugabannin soji zai ƙara wa jama’a kwarin gwiwa tare da ƙarfafa amincewa da matakan tsaro da ake ɗauka.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi
Next Post: Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan

Karin Labarai Masu Alaka

Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
Mataimakin Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wasu Wakilai Amurka
Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.