Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos
Published: April 2, 2026 at 1:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban Hafsan Sojin Ƙasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, a ranar Alhamis 2 ga Afrilu, 2026, ya jagoranci shugabannin hukumomin tsaro domin duba halin tsaro kai tsaye a birnin Jos na jihar Filato

Mukaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji, Kanal Appolonia Anele, ta bayyana a wata sanarwa cewa ziyarar na daga cikin ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da tabbatar da dorewar sa a faɗin jihar.

Sanarwar ta ce, bayan isowarsa ya samu tarba daga gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, a matsayin alamar kyakkyawar haɗin gwiwa tsakanin farar hula da sojoji wajen magance matsalolin tsaro.

Haka kuma, COAS ya karɓi cikakken bayani kan ayyukan tsaro daga Babban Kwamandan Runduna ta 3 da kuma Kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta Operation ENDURING PEACE, Manjo Janar Folusho Oyinlola, wanda ya yi bayani kan matakan da ake ɗauka tare da sauran hukumomin tsaro domin dakile barazana, kare rayuka da dukiyoyi, da kuma daidaita al’ummomin da abin ya shafa.

A yayin ziyarar, Laftanar Janar Waidi Shaibu ya gana da shugabannin al’umma da mazauna yankin, inda ya tabbatar musu da ƙudirin rundunar sojin kasa ta Najeriya na kare rayukan dukkan ‘yan ƙasa masu bin doka.

Ya kuma buƙaci al’umma su kasance cikin natsuwa da taka-tsantsan, su kuma mara wa hukumomin tsaro baya ta hanyar bin dokar takaita zirga-zirga (curfew) da kuma ba da cikakken haɗin kai a ayyukan bincike da tsaro, yayin da suke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Shugaban ƙaramar hukumar Jos ta Arewa, Mr. Dachung Bagos, ya yaba da ziyarar COAS, yana mai cewa zuwan manyan shugabannin soji zai ƙara wa jama’a kwarin gwiwa tare da ƙarfafa amincewa da matakan tsaro da ake ɗauka.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi
Next Post: Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan

Karin Labarai Masu Alaka

Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
  • Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Mataimakin Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wasu Wakilai Amurka
  • Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.