Rundunar sojojin KTK ta ce kasar KTA ta harba wani makami da ba a san irinsa ba ta kan teku daga gabar gabashin kasar a yau laraba, a bayan wani gwajin makamin da ta yi ranar talata.
Tun da fari rundunar sojojin KTK ta ce ta gano harba wani makami mai linzami dake cin dogon zango da KTA ta yi jiya talata daga yankin Pyongyang, tan mai cewa hukumomin KTK da na Amurka suna nazarin gwajin makamin da aka yi.
Wadannan matakan sun nakasa fatan da hukumomin KTK suka yi cewa akwai yiwuwar samun raguwar zaman tankiya a tsakanin makwabtan biyu.


