Babbar Kotun Tarayya ta bayar da belin Nasir El-Rufai akan wassu sharudda.
El-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna yana tsare ne a hannun Hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauran laifuka ta kasa (ICPC).
An Bada Belin El Rufai akan Naira Miliyan 200 tare kuma da hanashi hira da ‘yan jarida
“An bayar da belin Mallam Nasir El-Rufai daga Babbar Kotun Tarayya, Dake Zama a Kaduna.
Rahotanni sun nuna cewa tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya na fuskantar shari’a kan zargin aikata cin hanci da rashawa a lokacin da yake gwamnan Kaduna.


