Al’ummar yankin Mushere dake karamar hukumar Bokkos a jihar Filato sun bukaci gwamnatin jihar da tabi matakan da dokar kasa da ta ayyana, waje dawo musu da babban hakiminsu da ta Sauke daga sarauta.
Kimanin makonni biyu da suka gabata ne gwamnatin jihar Filato ta tumbuke babban hakimin yankin Mushere a karamar hukumar Bakkos a jihar Filato, Dakta Julius Dibilang, lamarin da ya janyo zanga-zanga da matan yankin suka yi tsirara.
Shugaban kungiyar raya al’ummar Mushere, Duwaf Bosco yace al’ummar yankin basu fahimci hujjar da gwamnati ta bayar na cire sarkin nasu ba.
Yankin na Mushere, inda tsohon gwamnan jihar Filato, Sanata Joshua Dariye ya fito, yayi shekaru bakwai babu hakimi, tun bayan rasuwar tsohon hakimin a shekarar dubu biyu da goma sha takwas, kafin a watan satumban bara, gwamnatin jihar ta nada Dakta Julius Dibilang a matsayin babban hakimin yankin.
Daya daga cikin matan da suka yi zanga-zanga kan cire sarkin tace yanzu sun kasance ba jagora, don haka zasu fuskanci matsaloli da dama.
To sai dai a bangaren gwamnati, gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa sun sami hakimin da laifin da kotu ta yanke masa hukunci da bai bayyana ba har sai bayan da aka bashi takarda.
Gwamnan ya kara da cewa, bayan sun sami shaidu masu gamsarwa daga wadanda suka yi korafin nada sarkin, ya zamo dole gwamnati ta janye takardar amincewa da sarautar, saboda doka ta haramta wa duk wanda kotu ta same shi da laifi rike ko wani irin mukami, har sai kotun ta warware hukuncin.
A halin da ake ciki dai, cire hakimin na Mushere ya janyo rarrabuwar kawunan al’ummar yankin, wanda wassu bayanai ke nuni da cewa bisa al’ada, ba zai yiwu a sake zaben wani sarki ba, har sai wannan sarkin ya bar duniya, yayinda wassu ke cewa za’a iya zaben wani hakimin ya maye gurbinsa.
Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos


