Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere
Published: April 20, 2026 at 2:01 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Al’ummar yankin Mushere dake karamar hukumar Bokkos a jihar Filato sun bukaci gwamnatin jihar da tabi matakan da dokar kasa da ta ayyana, waje dawo musu da babban hakiminsu da ta Sauke daga sarauta.

Kimanin makonni biyu da suka gabata ne gwamnatin jihar Filato ta tumbuke babban hakimin yankin Mushere a karamar hukumar Bakkos a jihar Filato, Dakta Julius Dibilang, lamarin da ya janyo zanga-zanga da matan yankin suka yi tsirara.

Shugaban kungiyar raya al’ummar Mushere, Duwaf Bosco yace al’ummar yankin basu fahimci hujjar da gwamnati ta bayar na cire sarkin nasu ba.

Yankin na Mushere, inda tsohon gwamnan jihar Filato, Sanata Joshua Dariye ya fito, yayi shekaru bakwai babu hakimi, tun bayan rasuwar tsohon hakimin a shekarar dubu biyu da goma sha takwas, kafin a watan satumban bara, gwamnatin jihar ta nada Dakta Julius Dibilang a matsayin babban hakimin yankin.

Daya daga cikin matan da suka yi zanga-zanga kan cire sarkin tace yanzu sun kasance ba jagora, don haka zasu fuskanci matsaloli da dama.

To sai dai a bangaren gwamnati, gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa sun sami hakimin da laifin da kotu ta yanke masa hukunci da bai bayyana ba har sai bayan da aka bashi takarda.

Gwamnan ya kara da cewa, bayan sun sami shaidu masu gamsarwa daga wadanda suka yi korafin nada sarkin, ya zamo dole gwamnati ta janye takardar amincewa da sarautar, saboda doka ta haramta wa duk wanda kotu ta same shi da laifi rike ko wani irin mukami, har sai kotun ta warware hukuncin.

A halin da ake ciki dai, cire hakimin na Mushere ya janyo rarrabuwar kawunan al’ummar yankin, wanda wassu bayanai ke nuni da cewa bisa al’ada, ba zai yiwu a sake zaben wani sarki ba, har sai wannan sarkin ya bar duniya, yayinda wassu ke cewa za’a iya zaben wani hakimin ya maye gurbinsa.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260420-WA0101.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
Next Post: An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado Afrika
Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • Jam’iyyar ADC Ta Karbi Peter Obi Da Wasu Manyan ‘Yan-Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.