Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere
Published: April 20, 2026 at 2:01 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Al’ummar yankin Mushere dake karamar hukumar Bokkos a jihar Filato sun bukaci gwamnatin jihar da tabi matakan da dokar kasa da ta ayyana, waje dawo musu da babban hakiminsu da ta Sauke daga sarauta.

Kimanin makonni biyu da suka gabata ne gwamnatin jihar Filato ta tumbuke babban hakimin yankin Mushere a karamar hukumar Bakkos a jihar Filato, Dakta Julius Dibilang, lamarin da ya janyo zanga-zanga da matan yankin suka yi tsirara.

Shugaban kungiyar raya al’ummar Mushere, Duwaf Bosco yace al’ummar yankin basu fahimci hujjar da gwamnati ta bayar na cire sarkin nasu ba.

Yankin na Mushere, inda tsohon gwamnan jihar Filato, Sanata Joshua Dariye ya fito, yayi shekaru bakwai babu hakimi, tun bayan rasuwar tsohon hakimin a shekarar dubu biyu da goma sha takwas, kafin a watan satumban bara, gwamnatin jihar ta nada Dakta Julius Dibilang a matsayin babban hakimin yankin.

Daya daga cikin matan da suka yi zanga-zanga kan cire sarkin tace yanzu sun kasance ba jagora, don haka zasu fuskanci matsaloli da dama.

To sai dai a bangaren gwamnati, gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa sun sami hakimin da laifin da kotu ta yanke masa hukunci da bai bayyana ba har sai bayan da aka bashi takarda.

Gwamnan ya kara da cewa, bayan sun sami shaidu masu gamsarwa daga wadanda suka yi korafin nada sarkin, ya zamo dole gwamnati ta janye takardar amincewa da sarautar, saboda doka ta haramta wa duk wanda kotu ta same shi da laifi rike ko wani irin mukami, har sai kotun ta warware hukuncin.

A halin da ake ciki dai, cire hakimin na Mushere ya janyo rarrabuwar kawunan al’ummar yankin, wanda wassu bayanai ke nuni da cewa bisa al’ada, ba zai yiwu a sake zaben wani sarki ba, har sai wannan sarkin ya bar duniya, yayinda wassu ke cewa za’a iya zaben wani hakimin ya maye gurbinsa.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260420-WA0101.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
Harin Ukraine Yayi Mummunan Barna A Rasha Afrika
Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika
Shugaban Amurka Ya Sauke Antoni Janar Amurka
Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.