Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
Published: April 22, 2026 at 8:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da fitar da kudi naira biliyan 17 domin gudanar da wani babban shiri na samar da ci gaba a matakin mazabu (Wards) da ke faɗin ƙasar nan.

​Wannan tallafi, wanda aka yi wa laƙabi da “Community-Based National Social Action Fund”, an kafa shi ne domin taba rayuwar talakawa kai-tsaye a dukkanin mazabu 8,804 na Najeriya, ta hanyar ba su damar gudanar da ayyukan da suka fi damunsu a yankunansu.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Lafiya da Walwalar Jama’a ta Tarayya ta fitar ranar Laraba, wadda mataimakin daraktan yaɗa labarai, Ado Bako ya sanya wa hannu, an bayyana cewa kowace mazaba za ta haɗa gwiwa ne da ƙungiyoyin sa-kai na cikin gida (CBOs) domin gano ayyukan da suka fi buƙata.

​Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya bayyana cewa wannan sabon salo ne na mika mulki ga talakawa. Ya ce, “Wannan tsari ya sanya al’umma a gaba wajen neman ci gaba. Ta hanyar barin kowace mazaba ta zaɓi abin da ya fi damunta, muna buɗe hanyoyin samar da maslaha da za su inganta rayuwa da kuma ayyukan gwamnati a inda aka fi buƙata.”

Sanarwar ta nuna cewa za a kashe kuɗaɗen ne a fannonin da suka haɗa da​Samar da abinci mai gina jiki ga al’umma, ​Samar da magunguna da kayayyakin kiwon lafiya, ​Gyaran makarantu, asibitoci, da samar da tsarin tsaftar muhalli.

​An tsara cewa za a fara aiwatar da wannan shiri ne daga ranar 1 ga watan Maris, 2026 zuwa watan Disambar 2026, inda Ma’aikatar Kuɗi da Ofishin Akanta-Janar na Ƙasa za su kula da asusun da aka ware wa shirin.

A wani labarin kuma mai alaƙa da wannan, Shugaba Tinubu ya amince da ɗaga matsayin Cibiyar Horar da Masu Maganin Kanjamau da Kuturta ta Ƙasa (NTBLTC) da ke Zariya, zuwa matsayin Babbar Cibiyar Bincike da Kula Lafiyar Jama’a da Cututtuka Masu Yaduwa (National Institute of Public Health and Infectious Diseases).

​Wannan mataki na nufin mayar da cibiyar ta Zariya ta zama tungar bincike, horarwa, da kuma shirin taryar duk wata annoba ko barazanar cututtuka da ka iya ɓallowa a ƙasar nan.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa
Next Post: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
Shugaba Trump Yace Akwai Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 30 A Jihar Neja Najeriya
  • Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago Tsaro
  • Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.