Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai

Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya.
Published: April 23, 2026 at 6:18 PM | By: Bala Hassan

Peter Obi, da Gwamnan Bauchi zasu hada kai don nemo hanyoyin da za’a warware matsalolin Nijeriya kafin zaben 2027
Daga Ahmad Muhammad,Bauchi

Tsohon Gwamnan Jihar Anambra Kuma tsohon dan Takarar Shugaban ƙasa a Jam’iyyar Labour Party Chief Peter Obi ya gayyaci Gwamnan Jihar Bauchi Sanata Bala Abdulqadir Mohammed Kan yazo su hada kai suyi aikin. Gyara Nijeriya.

Da yake amsa tambayoyin manema labarai Obi yace Wajibine a garemu mu ceto Nijeriya saboda yanayin halin da ake ciki Bai dace da rayuwarmu da rayuwar ‘ya’yanmu da jikokinmu ba.

“Na zo ne domin neman goyon bayan Gwamna Bala Mohammed da daukacin yankin Arewa maso Gabas yayin da muke kokarin tabbatar da hadin kan kasa. A halin yanzu, kasar nan tana kan hanya mara kyau, kuma yana da muhimmanci mu dauki matakai na gaggawa domin gyara alqiblar da muke kai.”

 

Obi ya ce ziyarar tana da nufin havaka haɗin kai da ƙarfafa haɗin gwiwa a faɗin ƙasar.

“Manufata ita ce neman goyon baya da haɗin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki, musamman daga jihar Bauchi da arewa maso Gabas,a cikin ƙoƙarinmu na haɗa kan wannan ƙasar,”

Ya yi watsi da jita-jitar da ake yi game da sauya sheƙa a siyasance, yana mai dagewa cewa batun da sukeyi ba wai game da haɗakar jam’iyya ba ne. “Ba ma gayyatar junanmu zuwa jam’iyyun siyasa ba; Muna gayyatar kanmu NE don mu gina ingantacciyar Najeriya,”

Yace abin damuwa ne ace Yau manomi ba Zai Iya zuwa Gona lafiya ba, xalibai basa Iya zuwa makaranta suyi karatu, baza ka Iya tafiya daga wannan gari zuwa wancan Garin ba Sai a Kamaka ace Sai ka Biya Kuxin fansa.
Ga Tarin matsalolin tsaro matsalolin tattalin arziki da sukayi tarnaqi wa rayuwar al’umma Wanda ya zamo dole muhaxa kai da sauran ‘yan Nijeriya don aceto qasarnan yadda za’a Samu ci gaba da kuma Zaman lafiya sannan a samu makoma Mai kyau da Zai yaqi yunwa, Talauci, rashin tsaro, rashin ingancin tattalin arziki da sauransu dole ne mu tsaya mu warware waxannan matsaloli da sukayi mana tarnaqi.

Da yake maida Jawabi ,Gwamnan Bauchi Sanata Bala Abdulqadir Mohammed ya godewa Peter Obi saboda wannan ziyarar yace Wajibine SU haxa kansu a siyasance don a Samu mafita Mai xorewa wa qasarnan.
Gwamna Bala yace su da suke vangaren adawa Wajibine SU nemi inuwar da zasu haxa kai su tafi tare domin ceto qasarnan.

 

Gwamna Bala ya ce yanzu shi “dan siyasa ne mai zaman kansa” ba tare da wata alaqa ta kai tsaye da kowace jam’iyya ba.

Gwamnan ya ce taron ya mayar da hankali kan haxin kan qasa da haxin gwiwa, yana mai cewa tattaunawar ba ta dogara ne da muradun jam’iyya ba. “PDP ko ADC ba sa tsayawa ni kaxai.
Ni xan siyasa ne mai zaman kansa yanzu, kuma jam’iyyarsa ma tana cikin ruxani. Muna duba vangaren shari’a. “Tabbas, dukkanmu muna cikin jam’iyyar adawa, kuma shi ya sa na ce wannan tattaunawa ce ta siyasa. Ba za mu bayyana duk abin da muka tattauna da yadda zamuyi ba.

Ya qara da cewa ci gaba da tattaunawa tsakanin masu ruwa da tsaki na siyasa ya mayar da hankali ne kan yiwuwar sake haxewa da haxin gwiwa kafin zave mai zuwa. “Ba za mu iya aiki ba tare da wani dandamali ba.” A ƙarshe, yanayin siyasa na yanzu na iya taimakawa wajen haɗa kanmu da kuma ƙarfafa damarmu ta cin zaɓe,” in ji shi.

Gwamnan ya bayyana ziyarar Obi a matsayin alama, na qarfafa guiwa,kuma yazo da tocila mai haskaka mana hanya.

” Saboda Yana magana ne game da haɗa kan ƙasar, , da kuma ƙirƙirar rayuwa Mai kyau ga Najeriya. Wannan shine abin da muke tsayawa a kai a matsayinmu na jiha da kuma a matsayinmu na mutane.
Muna jin daɗin wannan ziyarar sosai,” in ji Gwamnan.

 

in ji shi. Taron ya samu halartar masu ruwa da tsaki da dama a Kudu maso Gabas, ciki har da tsohon gwamnan jihar Imo, Achike Udenwa, da Sanata Enyinnaya Abaribe da Victor Umeh.

Wannan ziyarar yazo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shawarwari kan siyasa da Neman mafita kan makomar siyasan Gwamnan da magoya bayansa, tun bayan lokacin da Shugaban Jamiyyar PDP yace sun dakatar da tattaunawa da Jamiyyar APC, Kuma Abaya a cikin ‘yan watannin nan ya karvi baquncin masu ruwa da tsaki a dukkan fannoni na jam’iyya, ciki har da wakilin Shugaban Jamiyyar ADC DA Shugaban Jamiyyar APC , Jam’iyyun PRP DA NDC Suna ci gaba da yayin da ake qoqarin inda zaa Sami daidaito kafin zaven 2027.

Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516

Karin Labarai Masu Alaka

Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya.
  • Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe
  • Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.