Tun bayan da gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya ayyana Sanata Aliyu Wadada a matsayin wanda ya ke so ya gaje shi a kujerar gwamna, kasancewar ya kammala shekaru takwas da doka ta kayyade, al’ummar jihar ke ta cecekuce kan dacewa da rashin dacewar zabin na gwamna.

Aliyu Wadada wanda Sanata ne a majalisar dattawan Najeriya, ya ci zabe ne a karkashin jami’iyyar SDP, bayan ya shanza sheka daga jami’iyyar APC, kafin daga bisani ya sake komawa jami’iyyar ta APC.
Shugaban jam’iyyar APC a jihar Nasarawa, Honarabul Aliyu Bello yace ba abin tashin hankali bane don gwamna ya fadi ra’ayinsa.
Shiko Dadda’u Mamuda dan jami’iyyar APC ne a jihar Nasarawa, ya bayyana rashin amincewa da matakin gwamnan na fidda Sanata Aliyu Wadada a matsayin dan takara.
A gefe guda kuwa, mataimaki na musamman ga Sanata Aliyu Wadada a kan harkokin watsa labarai, Musa Umar Aboki yace gwamnan bai yi zaben tumun dare ba, saboda Aliyu Wadada masanin harkokin siyasa ne kuma yana da tarin magoya baya.
Abin jira a gani shine yadda zata kaya kafin zaben dubu biyu da ishirin da bakwai.
Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos


