Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci
Published: April 27, 2026 at 10:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta na yaƙi da talauci tare da samar da hanyoyin inganta rayuwar ’yan ƙasa, musamman ma mazauna karkara waɗanda ayyukan ci gaba ba su cika isa gare su ba.

Babban Manajan Shirin GEEP 3.0 na “FarmerMoni” karkashin tsarin ‘Renewed Hope’, Hamza Ibrahim-Baba, shi ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin taron wayar da kan kafofin yaɗa labarai na shiyyar Arewa maso Yamma da aka gudanar a birnin Kano.

Ibrahim-Baba ya bayyana cewa wannan shiri na RH-GEEP 3.0, wanda ya shafi manoman rani da na damina, wani ɓangare ne na manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na farfaɗo da tattalin arziƙin ƙananan sana’o’i a faɗin ƙasar nan.

Ya ce: “An tsara GEEP 3.0 ne domin ya isa zuwa ga al’ummar da aka bari a baya, da kuma inganta tattalin arziƙi tun daga tushe. Burinmu shi ne mu tallafa wa ’yan Nijeriya da ke can ƙasan matattarar tattalin arziƙi, mu inganta rayuwarsu, kuma mu samar musu da damar samun kudin shiga mai dorewa.”

A nata jawabin, Darakta Janar ta Hukumar Kare Muradin Jama’a ta Jihar Kano, Fatima Abubakar-Abdullahi, ta bayyana cewa shirin ya sa gaba ne wajen tallafa wa rukunin mutanen da suka fi rauni, musamman manoma da ƙananan ’yan kasuwa na karkara.

Ta ƙara da cewa shirin zai samar da damar samun rance ba tare da ruwa ba, tare da bayar da horon gina ƙwarewa ga masu cin gajiyar shirin.

Haka zalika, ta jaddada mahimmancin wayar da kai, inda ta nuna cewa da yawa daga cikin waɗanda suka cancanci shirin ba su riga sun fahimci hanyoyin da za su bi domin cin gajiyar sa ba.

“Irin wannan wayar da kan na da mahimmanci matuƙa. Idan mutane suka fahimci yadda shirin yake tafiya, shiga cikinsa zai ƙaru, sannan tasirinsa zai kasance mai ma’ana ga rayuwarsu,” in ji ta.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci
Next Post: Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Zai Dakatar Da Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
Sakamakon Yakin Gabas Ta Tsakiya Kowacce Gangar Mai Ta Haura Dala 100 Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci
  • Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai
  • Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila Afrika
  • Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.