Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu
Published: May 7, 2026 at 7:45 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar Alhamis 7 ga watan Mayu ne, Mataimakin Shugaban Najeriya Kashim Shettima ya kaddamar da neman takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a hukumance ga uwar jam’iyyar APC ta kasa.

A wani gagarumin taro da aka gudanar a dakin taro na *Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre* Mataimakin ya jagoranci mambobin jam’iyyar da suka hada da gwamnoni, da yan majalisun tarayya, da sauran masu madafun iko na da da na yanzu, inda ya miƙa fom din neman takarar ga Shugabannin jam’iyyar a wani mataki na nuna goyon bayan masu madafun iko ga kudurin sake zaben shugaba Tinubu zango na biyu.

Da yake jawabi jim kadan bayan mika fom din, Mataimakin Shugaban Kasa Shettima ya bayyana shugaban a matsayin jagora mai juriya wanda ya yi nasarar Jan ragamar Najeriya zuwa tudun-mun tsira a yayinda guguwar matsalolin tattalin arziki ta so yin awon gaba da ita. Kashim ya kafa hujja da ajandar “Renewed Hope” a matsayin babban dalilin cancantar Shugaba Tinubu ga zagaye na biyu inda ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin ta kawo sun fara samar da sakamako mai kyau, duk da tsaurin da suka zo da shi a karon farko.

“Kalubalen shekarun da suka gabata ba su raunana Shugaba Tinubu ba; maimakon haka ma sai kara masa kwarewa da suka yi,” in ji Shettima, inda ya ci gaba da cewa

“Wannan gwarzantaka da kwarewa da ya kara ne ya sa mu ke fatan kara masa wata dama”

A nata bangaren, uwar jam’iyyar ta kasa ta nuna cikakken goyon bayanta ga takarar, inda

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda wanda ya karbi takardun takarar, ya ce ayyukan shugaba Tinubu a sassa daban-daban na farfado da kasar sun sa sake zaben nasa ya zama dole.

Yilwatda ya yi nuni da kyautatuwar tattalin arziki da karuwar kwarin gwiwar kasashen duniya ga makomar Najeriya a matsayin hujjojin da jam’iyyar ta dogara da su wajen amincewa da takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Shi ma shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Tajudeen Abbas ya yaba da garambawul din na shugaban Tinubu, wanda ya bayyana a matsayin harsashin farfadowar kasa mai dorewa.

Ita ma kungiyar Gwamnonin APC ta bakin Shugabanta kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma wanda gwamnoni 12 suka rufa wa baya ta nuna goyon baya na bai-daya ga takarar

Gwamnonin da suka halarci taron su ne na jihohin Plateau, Ogun, Niger, Kaduna, Ondo, Katsina, Borno, Cross River, Taraba, Yobe, Nasarawa, da Bayelsa.

A yanzu dai mika tikitin takarar a hukumance ya kawo karshen rade-raden da ake yi game da aniyar shugaban ta neman wa’adin Mulki na biyu kamar yadda ta bayyana irin hadin kan Shugabanni na bai daya da ake dakon gani a zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC.

Shugabannin jam’iyyar sun yi kira ga mambobinsu da su fito ƙwansu da ƙwarƙwatarsu don “kare fatan Najeriya.”.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina
Next Post: Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP Afrika
Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Sabon Ministan Kudi Labarai
  • Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
  • Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.