Gwamnatin Tarayya ta sanar da shirin kashe kudi kusan naira biliyan 250 a cikin shekarar 2026 domin gina sabbin dakunan kwanan dalibai a manyan makarantun gaba da sakandare na kasar.
Wannan mataki na kunshe ne a cikin wani babban shiri na kyautata jin dadin dalibai da kuma fadada damar samun ilimi mai inganci, wanda ake ganin shi ne jari mafi tsoka da aka taba zubawa a fannin gidajen dalibai a tarihin Najeriya.
Ministan Ilimi, Maruf Olatunji Alausa, ya bayyana cewa wannan shiri zai magance matsalolin karancin masauki da dalibai ke fuskanta.
Za a kashe naira biliyan 100 wajen gina dakunan kwanan dalibai masu dauke da gado 500 a kowace jami’a daga jami’o’i guda 50 a fadin kasar nan. Kowanne aiki daya an kiyasta shi a kan naira biliyan 2.
Za a gudanar da wasu ayyukan guda 24 na hadin gwiwa da masu zuba jari masu zaman kansu, inda gwamnati za ta bayar da biliyan daya, su kuma masu zuba jari su bayar da biliyan 3 a kowanne aiki. Wannan zai samar da masauki ga dalibai tsakanin 1,200 zuwa 1,500 a kowace makaranta.
Hukumar tallafawa manyan makarantu ta TETFund ce za ta dauki nauyin samar da wadannan kudade, inda za a yi amfani da su wajen gina sabbi da kuma gyara tsofaffin dakunan kwanan dalibai da suka lalace.
Babban burin wannan shiri shi ne samar da yanayi mai kyau na koyo da koyarwa, tare da rage cinkoson dalibai a daki daya da ake samu a manyan makarantun kasar nan a halin yanzu.
“Wannan shiri ne da zai tabbatar da cewa dalibanmu sun samu wurin kwana mai tsafta da walwala, wanda hakan zai taimaka musu wajen mayar da hankali kan karatunsu.” — Maruf Olatunji Alausa
Masana ilimi sun yi amanna cewa idan har aka kammala wadannan ayyuka, za a samu sauki kwarai wajen rage kuncin da daliban jami’o’i da kwalejoji ke fuskanta, musamman ‘ya’yan talakawa da ke dogara da masaukin makaranta.


