Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
Published: May 12, 2026 at 8:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta sanar da shirin kashe kudi kusan naira biliyan 250 a cikin shekarar 2026 domin gina sabbin dakunan kwanan dalibai a manyan makarantun gaba da sakandare na kasar.

Wannan mataki na kunshe ne a cikin wani babban shiri na kyautata jin dadin dalibai da kuma fadada damar samun ilimi mai inganci, wanda ake ganin shi ne jari mafi tsoka da aka taba zubawa a fannin gidajen dalibai a tarihin Najeriya.

Ministan Ilimi, Maruf Olatunji Alausa, ya bayyana cewa wannan shiri zai magance matsalolin karancin masauki da dalibai ke fuskanta.

Za a kashe naira biliyan 100 wajen gina dakunan kwanan dalibai masu dauke da gado 500 a kowace jami’a daga jami’o’i guda 50 a fadin kasar nan. Kowanne aiki daya an kiyasta shi a kan naira biliyan 2.

Za a gudanar da wasu ayyukan guda 24 na hadin gwiwa da masu zuba jari masu zaman kansu, inda gwamnati za ta bayar da biliyan daya, su kuma masu zuba jari su bayar da biliyan 3 a kowanne aiki. Wannan zai samar da masauki ga dalibai tsakanin 1,200 zuwa 1,500 a kowace makaranta.

Hukumar tallafawa manyan makarantu ta TETFund ce za ta dauki nauyin samar da wadannan kudade, inda za a yi amfani da su wajen gina sabbi da kuma gyara tsofaffin dakunan kwanan dalibai da suka lalace.

Babban burin wannan shiri shi ne samar da yanayi mai kyau na koyo da koyarwa, tare da rage cinkoson dalibai a daki daya da ake samu a manyan makarantun kasar nan a halin yanzu.

“Wannan shiri ne da zai tabbatar da cewa dalibanmu sun samu wurin kwana mai tsafta da walwala, wanda hakan zai taimaka musu wajen mayar da hankali kan karatunsu.” — Maruf Olatunji Alausa

Masana ilimi sun yi amanna cewa idan har aka kammala wadannan ayyuka, za a samu sauki kwarai wajen rage kuncin da daliban jami’o’i da kwalejoji ke fuskanta, musamman ‘ya’yan talakawa da ke dogara da masaukin makaranta.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi
Next Post: Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030 Labarai
Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
  • Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
  • Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
  • Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli Afrika
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.