Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana shirinta na yin aiki kafada da kafada da ƙasar Poland wajen inganta harkokin tsaron cikin gida da bunƙasa tattalin arziki.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi Mataimakin Firaministan Poland, Krzysztof Gawkowski, a ofishinsa da ke Abuja ranar Alhamis.
Tunji-Ojo ya ce Najeriya na da burin anfani da ƙwarewar Poland wajen kula da iyakoki da kuma dabarun tsaron cikin gida da suka tabbatar da nasara a ƙasar.
Ya ce gwamnatin Najeriya na sa ran yin haɗin gwiwa da Poland musamman a fannoni kamar horas da jami’ai, amfani da fasaha, tsaron yanar gizo da sauran muhimman fannoni.
“Mun yi imani cewa haɗin kai da koyo daga juna ne hanya mafi dacewa wajen rage rauninmu tare da ƙarfafa bangarorin da muke da ƙwarewa,” in ji shi.
Ministan ya tabbatar wa baƙin cewa ziyarar ba za ta zama ta al’ada kawai ba, domin za ta zama tubalin da za a gina dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu.
Ya kuma bayyana cewa ana shirye-shiryen kai ziyara ƙasar Poland domin ƙara zurfafa tattaunawa da gwamnatin ƙasar da kuma ɓangaren kasuwanci masu alaƙa da ma’aikatar harkokin cikin gida.
Tunji-Ojo ya ƙara da cewa manufofin tattalin arzikin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na nuna cewa gwamnati na fahimtar hanyoyin gina tattalin arziki mai ƙarfi.
A nasa jawabin, Mataimakin Firaministan Poland, wanda kuma shi ne Ministan Harkokin Dijital na ƙasar, Krzysztof Gawkowski, ya ce Najeriya ƙasa ce mai tarin albarkatun tattalin arziki, yawan jama’a da kuma damar ci gaban fasaha.
Ya bayyana Najeriya a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗa wajen gina dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu.
Gawkowski ya ce Poland a shirye take ta taimaka wa Najeriya ta hanyar ƙwarewarta a fannoni kamar kirkire-kirkire, fasahar zamani, gina ababen more rayuwa da kuma sabbin dabarun fasaha.
Haka kuma ya bayyana fatan ganin Ministan Harkokin Cikin Gida na Najeriya ya kai ziyara Poland domin ƙara ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu.


