Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Najeriya Da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki
Published: May 21, 2026 at 2:18 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana shirinta na yin aiki kafada da kafada da ƙasar Poland wajen inganta harkokin tsaron cikin gida da bunƙasa tattalin arziki.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi Mataimakin Firaministan Poland, Krzysztof Gawkowski, a ofishinsa da ke Abuja ranar Alhamis.

Tunji-Ojo ya ce Najeriya na da burin anfani da ƙwarewar Poland wajen kula da iyakoki da kuma dabarun tsaron cikin gida da suka tabbatar da nasara a ƙasar.

Ya ce gwamnatin Najeriya na sa ran yin haɗin gwiwa da Poland musamman a fannoni kamar horas da jami’ai, amfani da fasaha, tsaron yanar gizo da sauran muhimman fannoni.

“Mun yi imani cewa haɗin kai da koyo daga juna ne hanya mafi dacewa wajen rage rauninmu tare da ƙarfafa bangarorin da muke da ƙwarewa,” in ji shi.

Ministan ya tabbatar wa baƙin cewa ziyarar ba za ta zama ta al’ada kawai ba, domin za ta zama tubalin da za a gina dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu.

Ya kuma bayyana cewa ana shirye-shiryen kai ziyara ƙasar Poland domin ƙara zurfafa tattaunawa da gwamnatin ƙasar da kuma ɓangaren kasuwanci masu alaƙa da ma’aikatar harkokin cikin gida.

Tunji-Ojo ya ƙara da cewa manufofin tattalin arzikin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na nuna cewa gwamnati na fahimtar hanyoyin gina tattalin arziki mai ƙarfi.

A nasa jawabin, Mataimakin Firaministan Poland, wanda kuma shi ne Ministan Harkokin Dijital na ƙasar, Krzysztof Gawkowski, ya ce Najeriya ƙasa ce mai tarin albarkatun tattalin arziki, yawan jama’a da kuma damar ci gaban fasaha.

Ya bayyana Najeriya a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗa wajen gina dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu.

Gawkowski ya ce Poland a shirye take ta taimaka wa Najeriya ta hanyar ƙwarewarta a fannoni kamar kirkire-kirkire, fasahar zamani, gina ababen more rayuwa da kuma sabbin dabarun fasaha.

Haka kuma ya bayyana fatan ganin Ministan Harkokin Cikin Gida na Najeriya ya kai ziyara Poland domin ƙara ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani
Next Post: Jam’iyyar APC Ta Ayana Jamilu Gwamna A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya
Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
  • Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.