Jam’iyyar APC a jihar Gombe ta ayana Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin ɗan takararta na gwamna domin babban zaɓen shekarar 2027, bayan nasarar da ya samu a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar.
Sakamakon zaɓen da kwamitin gudanarwa ya sanar ya nuna cewa Dakta Jamilu Gwamna ya samu ƙuri’u 247,161, inda ya kayar da sauran ‘yan takarar biyu da suka fafata a zaɓen.
Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya samu ƙuri’u 12,120, yayin da tsohon Ministan Sufuri, Sanata Said Ahmed Alkali, ya samu ƙuri’u 11,612.
Shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna, Sanata Sani Danladi, ya bayyana cewa an gudanar da zaɓen cikin lumana tare da bin ƙa’idojin jam’iyyar da tanade-tanaden dokar zaɓe.
Ya kuma yaba wa mambobin jam’iyyar APC a faɗin jihar bisa yadda suka fito domin kaɗa ƙuri’a cikin tsari da lumana, yana mai cewa hakan alama ce ta haɗin kai da ƙarfin jam’iyyar a jihar Gombe.
An sanar da sakamakon ne a sakatariyar jam’iyyar APC da ke Gombe, a gaban jami’an hukumar zaɓe ta ƙasa INEC, masu sa ido kan zaɓe, jami’an tsaro, kafafen yaɗa labarai da kuma manyan jami’an jam’iyyar.


