Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziƙin Zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya koma jam’iyyar Peoples Democratic Party tare da samun tikitin takarar gwamna na jam’iyyar a jihar Gombe.
Pantami ya samu nasarar ne ta hanyar amincewar baki ɗaya daga mambobin jam’iyyar yayin zaɓen fidda gwani da aka gudanar ranar Talata a Gombe.
Shugaban Kwamitin Zaɓen Fidda Gwanin na PDP, Gregory Yenlong, ne ya bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen kasancewar shi kaɗai ne ɗan takarar da ya tsaya takara.
Da yake jawabi jim kaɗan bayan ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara, Pantami ya ce ya shiga takarar ne domin yi wa al’ummar jihar Gombe hidima.
Ya kuma yi alƙawarin gudanar da mulki cikin adalci da gaskiya ga al’ummar jihar idan aka zaɓe shi a matsayin gwamna.


