Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika

Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP
Published: May 26, 2026 at 1:23 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 26, 2026

Wani jigo a jam’iyyar PDP a jihar Gombe, kuma ɗaya daga cikin masu neman tikitin takarar gwamna, Alhaji Abdulkadir Hamma Saleh, ya bayyana rashin amincewarsa da matakin jam’iyyar na bai wa Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami tikitin takarar gwamna.

Da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke Gombe, Hamma Saleh ya ce sun shafe shekaru suna yi wa jam’iyyar hidima tare da jajircewa, don haka ba za su amince da yadda aka bayyana Pantami a matsayin ɗan takarar gwamna ba tare da sahihin bayani ga masu ruwa da tsaki ba.

Ya ce ba su da wata masaniya dangane da shigowar Pantami cikin jam’iyyar PDP, illa dai kawai suka ji an bayyana shi a matsayin ɗan takarar gwamna.

Hamma Saleh ya ƙara da cewa zai bi duk hanyoyin da doka ta tanada domin kare haƙƙinsa, yana mai cewa shi cikakken ɗan jam’iyyar PDP ne wanda tun da farko ya sayi fom ɗin neman takarar gwamna.

Jigon ɗan siyasar ya kuma bayyana cewa sun san Malam Pantami ne a matsayin mamban jam’iyyar APC, kuma wanda ya taɓa neman tsayawa takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar amma bai samu nasara ba.

“Idan Yace ba’ayi mishi adalci a APC ba, to Shi yayi mana adalci” Inji Hamma Saleh.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP

Karin Labarai Masu Alaka

An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai
Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani. Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya Afrika
Pakistan Zata Karbi Bakwancin Saudiya, Turkiyya Da Masar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
  • IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12 Rediyo
  • Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito Afrika
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.