Wani jigo a jam’iyyar PDP a jihar Gombe, kuma ɗaya daga cikin masu neman tikitin takarar gwamna, Alhaji Abdulkadir Hamma Saleh, ya bayyana rashin amincewarsa da matakin jam’iyyar na bai wa Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami tikitin takarar gwamna.
Da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke Gombe, Hamma Saleh ya ce sun shafe shekaru suna yi wa jam’iyyar hidima tare da jajircewa, don haka ba za su amince da yadda aka bayyana Pantami a matsayin ɗan takarar gwamna ba tare da sahihin bayani ga masu ruwa da tsaki ba.
Ya ce ba su da wata masaniya dangane da shigowar Pantami cikin jam’iyyar PDP, illa dai kawai suka ji an bayyana shi a matsayin ɗan takarar gwamna.
Hamma Saleh ya ƙara da cewa zai bi duk hanyoyin da doka ta tanada domin kare haƙƙinsa, yana mai cewa shi cikakken ɗan jam’iyyar PDP ne wanda tun da farko ya sayi fom ɗin neman takarar gwamna.
Jigon ɗan siyasar ya kuma bayyana cewa sun san Malam Pantami ne a matsayin mamban jam’iyyar APC, kuma wanda ya taɓa neman tsayawa takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar amma bai samu nasara ba.
“Idan Yace ba’ayi mishi adalci a APC ba, to Shi yayi mana adalci” Inji Hamma Saleh.


