Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke
Published: November 28, 2025 at 2:14 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kungiyar CISLAC guda cikin kungiyoyin rajin shugabanci na gari a Najeriya, ta bukaci gwamnatin kasar ta janye sunan Mr. Ayodele Oke daga jerin sunayen mutanen data mikawa majalisar dattawan kasar, domin ta amince a nada su jakadun kasashen ketare.

A jiya laraba ne, shugaba Tinubu ya mikawa majalisar sunan Alhaji Aminu Dalhatu daga jihar Jigawa da Mr. Kayode Are daga jihar Ogun da kuma Mr. Ayodele Oke daga jihar Oyo, wadanda yake muradin nadawa Jakadun Najeriya a ketare.

Sai dai, Kungiyar ta CISLAC, ta bukaci hukumar tsaro ta farin kaya DSS, kada ta wanke Mr. Oke saboda hukumar EFCC na tuhumar sa a gaban kotu, saboda zargin yana da hannu shi da mai dakinsa akan wasu kudade da hukuma ke zargin cewa, na almundahana ne.

A cikin watan Afrilu na shekara ta 2019, hukumar ta EFCC ta gano kudaden fiye da dala miliyan 43 da kuma Fam na Ingila fiye da miliyan 27 a qani gida dake kan titin Osborne a Unguwar Ikoyi ta birnin Lagos.

Bayan kammala bincike hukumar ta gabatar da batun a gaban babbar kotun tarayya dake Lagos, tana mai zargin cewa, Mr. Ayodele Oke da mai dakinsa nada hannu wajen boye kudaden.

Mr. Ayodele Oke dake zaman tsohon shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta Najeriya NIA, ya ki amsa sammacin kotu lokacin da hukumar EFFC ta gurfanar dashi domin amsa tuhuma akan wadancam kudade data gano.

Shugaban kungiyar ta CISLAC Auwal Musa Rafsanjani ya fadawa manema labarai a Abuja cewa, kungiyar ta kadu da yunkurin nada mutanen da ake tuhuma da rashawa, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin kunya ga kasa kuma ka iya tauye kimar Najeriya a idon duniya.

Yanzu dai Najeriya ta shafe fiye da shekaru biyu ke nan, bata da Jakadun dake kula mata da harkokin diplomasiyya a kasashen waje.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Next Post: Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
Maulidi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Hutu Afrika
Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u Afrika
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.