Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke
Published: November 28, 2025 at 2:14 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kungiyar CISLAC guda cikin kungiyoyin rajin shugabanci na gari a Najeriya, ta bukaci gwamnatin kasar ta janye sunan Mr. Ayodele Oke daga jerin sunayen mutanen data mikawa majalisar dattawan kasar, domin ta amince a nada su jakadun kasashen ketare.

A jiya laraba ne, shugaba Tinubu ya mikawa majalisar sunan Alhaji Aminu Dalhatu daga jihar Jigawa da Mr. Kayode Are daga jihar Ogun da kuma Mr. Ayodele Oke daga jihar Oyo, wadanda yake muradin nadawa Jakadun Najeriya a ketare.

Sai dai, Kungiyar ta CISLAC, ta bukaci hukumar tsaro ta farin kaya DSS, kada ta wanke Mr. Oke saboda hukumar EFCC na tuhumar sa a gaban kotu, saboda zargin yana da hannu shi da mai dakinsa akan wasu kudade da hukuma ke zargin cewa, na almundahana ne.

A cikin watan Afrilu na shekara ta 2019, hukumar ta EFCC ta gano kudaden fiye da dala miliyan 43 da kuma Fam na Ingila fiye da miliyan 27 a qani gida dake kan titin Osborne a Unguwar Ikoyi ta birnin Lagos.

Bayan kammala bincike hukumar ta gabatar da batun a gaban babbar kotun tarayya dake Lagos, tana mai zargin cewa, Mr. Ayodele Oke da mai dakinsa nada hannu wajen boye kudaden.

Mr. Ayodele Oke dake zaman tsohon shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta Najeriya NIA, ya ki amsa sammacin kotu lokacin da hukumar EFFC ta gurfanar dashi domin amsa tuhuma akan wadancam kudade data gano.

Shugaban kungiyar ta CISLAC Auwal Musa Rafsanjani ya fadawa manema labarai a Abuja cewa, kungiyar ta kadu da yunkurin nada mutanen da ake tuhuma da rashawa, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin kunya ga kasa kuma ka iya tauye kimar Najeriya a idon duniya.

Yanzu dai Najeriya ta shafe fiye da shekaru biyu ke nan, bata da Jakadun dake kula mata da harkokin diplomasiyya a kasashen waje.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Next Post: Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora

Karin Labarai Masu Alaka

Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro Afrika
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
  • An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.