Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Afrika

NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai
Published: June 1, 2026 at 4:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Alhazai ta Kasar Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa za a fara jigilar alhazan Najeriya zuwa gida daga ranar 3 ga watan Yuni, tare da yin kira ga alhazai da su bi ka’idojin tafiye-tafiye domin kauce wa jinkiri.

Shugaban Sashen Ayyukan Jiragen Sama na hukumar, Alhaji Habib Bello, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a birnin Makkah.

Ya ce jadawalin tashin jiragen dawowa yana karkashin kamfanonin jiragen sama ne tare da amincewar Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Saudiyya (GACA), wadda ke ware lokutan tashin jirage ga kamfanoni daban-daban.

A cewar sa, kamfanin Max Air zai fara jigilar alhazan Jihar Nasarawa daga ranar 3 ga Yuni, yayin da Flynas da Air Peace za su fara jigilar alhazan jihohin Ogun da Oyo daga ranar 4 ga Yuni.

Bello ya ce an tanadi dokar daukar jakunkuna biyu masu nauyin kilo 23 kowanne da kuma jakar hannu mai nauyin kilo 8, yana mai gargadin cewa rashin bin wannan ka’ida na iya haifar da jinkirin tashi ko hana mahajjaci shiga jirgin.

Ya kuma bukaci alhazai da jami’an jihohi su sanar da hukumomi akalla sa’o’i 48 kafin ranar tafiyarsu domin saukaka shirye-shiryen fitar da fasfo, jigilar kaya da sauran muhimman matakai.

A nasa bangaren, Shugaban Kwamitin Fasfo na NAHCON a Makkah, Alhaji Abdurrahman Mohammed, ya ce an kammala matakin farko na aikin Hajjin bana cikin nasara, kuma an fara shirye-shiryen fitar da fasfofin alhazan da za su koma gida.

Ya bayyana cewa ana ajiye fasfofin alhazai ne domin kare su daga bacewa ko lalacewa, tare da tabbatar da saukin gudanar da harkokin tafiya.

Mohammed ya ce duk mahajjacin da ke shirin tafiya ya kamata ya gabatar da bayanansa akalla sa’o’i 48 kafin tashinsa domin a samu saukin fitar da fasfonsa da kuma shirya masa tafiya.

Ya tabbatar da cewa akwai matakan da aka tanada domin gano fasfofin da suka bace, yayin da za a samar da Takardar Tafiya ta Gaggawa (ETC) ga duk wanda ba a samu fasfonsa ba.

Jami’an biyu sun yi kira ga alhazai da jami’an kula da su da su ba da hadin kai domin tabbatar da cewa aikin dawo da alhazan Najeriya ya gudana cikin sauki da nasara.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani
Next Post: Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba Afrika
Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
  • Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
  • Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
  • Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka Amurka
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia Tsaro
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.