Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
  • NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Afrika

Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya
Published: June 3, 2026 at 1:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya (INEC), ta ce ta fara bincike kan zargin fitar da bayanan wani ɗan takara daga kundin rajistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR), yayin da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya, (DSS), ita ma ta fara nata binciken.

INEC ta bayyana cewa binciken farko ya nuna babu wani kutse daga waje ko harin na’ura mai kwakwalwa da ya shiga tsarin bayananta. Sai dai an samu damar shiga bayanan ne ta hanyar sahihan bayanan shiga da aka bai wa wasu jami’an rajistar masu zaɓe, amma aka fitar da bayanan ba tare da izini ba.

Hukumar ta ce ta gano asusun da aka yi amfani da shi wajen shiga bayanan, kuma tana binciken ko an karya dokokin tsaro da kariyar bayanai. Ta kuma tabbatar da cewa lamarin bai shafi bayanan sama da masu zaɓe miliyan 90 da ke cikin kundinta ba.

Sai dai ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya ce bayanin da INEC ta fitar ya ƙara haifar da tambayoyi fiye da amsoshi. Ya buƙaci a yi cikakken bincike domin gano yadda bayanan da ke cikin tsarin da aka killace suka kai hannun wasu ‘yan siyasa.

Atiku ya ce rashin samun kutse daga waje ba ya rage girman lamarin, domin hakan na nuna yiwuwar matsalar ta fito daga cikin tsarin hukumar. Ya kuma yi maraba da binciken DSS, yana mai cewa dole ne a gudanar da shi cikin adalci ba tare da nuna son kai ba.

Takaddamar ta samo asali ne bayan mai taimaka wa Ministan Abuja kan harkokin yaɗa labarai, Lere Olayinka, ya wallafa bayanan rajistar zaɓe na fitaccen jarumin Nollywood, Emeka Ike. Jarumin ya yi zargin cewa an karya masa haƙƙin sirri, tare da barazanar ɗaukar matakin shari’a kan lamarin.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai
Next Post: An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Ghana Ta Tono Gold Na Miliyoyin Kudade Kimiya
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.