Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya (INEC), ta ce ta fara bincike kan zargin fitar da bayanan wani ɗan takara daga kundin rajistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR), yayin da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya, (DSS), ita ma ta fara nata binciken.
INEC ta bayyana cewa binciken farko ya nuna babu wani kutse daga waje ko harin na’ura mai kwakwalwa da ya shiga tsarin bayananta. Sai dai an samu damar shiga bayanan ne ta hanyar sahihan bayanan shiga da aka bai wa wasu jami’an rajistar masu zaɓe, amma aka fitar da bayanan ba tare da izini ba.
Hukumar ta ce ta gano asusun da aka yi amfani da shi wajen shiga bayanan, kuma tana binciken ko an karya dokokin tsaro da kariyar bayanai. Ta kuma tabbatar da cewa lamarin bai shafi bayanan sama da masu zaɓe miliyan 90 da ke cikin kundinta ba.
Sai dai ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya ce bayanin da INEC ta fitar ya ƙara haifar da tambayoyi fiye da amsoshi. Ya buƙaci a yi cikakken bincike domin gano yadda bayanan da ke cikin tsarin da aka killace suka kai hannun wasu ‘yan siyasa.
Atiku ya ce rashin samun kutse daga waje ba ya rage girman lamarin, domin hakan na nuna yiwuwar matsalar ta fito daga cikin tsarin hukumar. Ya kuma yi maraba da binciken DSS, yana mai cewa dole ne a gudanar da shi cikin adalci ba tare da nuna son kai ba.
Takaddamar ta samo asali ne bayan mai taimaka wa Ministan Abuja kan harkokin yaɗa labarai, Lere Olayinka, ya wallafa bayanan rajistar zaɓe na fitaccen jarumin Nollywood, Emeka Ike. Jarumin ya yi zargin cewa an karya masa haƙƙin sirri, tare da barazanar ɗaukar matakin shari’a kan lamarin.


