Kungiyar Tarayyar Turai (EU) ta jinjina wa Amurka da Iran bayan amincewarsu da wata yarjejeniyar sulhu da ake sa ran za ta kawo karshen tashin hankalin da ya janyo asarar rayuka da dukiyoyi a yankin Gabas ta Tsakiya.
Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, ya bayyana cewa Iran ta amince da sabon daftarin yarjejeniyar tsagaita bude wuta, tare da sanar da cewa za a rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar 19 ga Yuni, 2026 a birnin Geneva na kasar Switzerland.
A nata bangaren, EU ta bayyana goyon bayanta ga yarjejeniyar, tare da jaddada aniyarta na ci gaba da bayar da gudunmawa wajen tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a yankin Gabas ta Tsakiya.


