Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta bayyana cewa ta lalata gonakin wiwi masu fadin sama da hekta 51 tare da kama mutane 281 da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, sayarwa da kuma amfani da su a jihar Ekiti cikin shekara guda.
Kwamandan NDLEA na jihar, Rufus Aina, ne ya bayyana hakan a Ado Ekiti yayin bikin Ranar Yaki da Miyagun Kwayoyi ta Duniya ta 2026.
Ya ce hukumar ta samu nasarar gurfanar da mutane 50 da aka yanke musu hukunci, yayin da sauran shari’o’i ke gaban Kotun Tarayya da ke Ado Ekiti.
Aina ya ce noman wiwi a sassa daban-daban na jihar na ci gaba da zama babban kalubale, yana mai gargadin cewa safara da amfani da miyagun kwayoyi na haddasa aikata laifuka, rashin tsaro, barin makaranta da kuma lalata rayuwar al’umma.
Ya kara da cewa cikin shekara guda da ta gabata, hukumar ta gudanar da gangamin wayar da kai 76 da shirye-shiryen rediyo da talabijin 15, tare da ba mutane 87 masu amfani da miyagun kwayoyi shawara da jinya.
Har ila yau, ya bayyana cewa an kwato miyagun kwayoyi masu nauyin kilogram 6,337.517, yayin da wani mutum mai suna Osho Akindele ya samu daurin shekaru 20 a gidan yari saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi.
Kwamandan ya kuma bayyana cewa an kama wasu tsofaffi biyu masu shekaru 78 da 80 bisa zargin mallaka da safarar miyagun kwayoyi, yana kira ga al’umma da su hada kai da hukumomi wajen yaki da matsalar miyagun kwayoyi.


