Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika

Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti
Published: June 26, 2026 at 9:28 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta bayyana cewa ta lalata gonakin wiwi masu fadin sama da hekta 51 tare da kama mutane 281 da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, sayarwa da kuma amfani da su a jihar Ekiti cikin shekara guda.

Kwamandan NDLEA na jihar, Rufus Aina, ne ya bayyana hakan a Ado Ekiti yayin bikin Ranar Yaki da Miyagun Kwayoyi ta Duniya ta 2026.

Ya ce hukumar ta samu nasarar gurfanar da mutane 50 da aka yanke musu hukunci, yayin da sauran shari’o’i ke gaban Kotun Tarayya da ke Ado Ekiti.

Aina ya ce noman wiwi a sassa daban-daban na jihar na ci gaba da zama babban kalubale, yana mai gargadin cewa safara da amfani da miyagun kwayoyi na haddasa aikata laifuka, rashin tsaro, barin makaranta da kuma lalata rayuwar al’umma.

Ya kara da cewa cikin shekara guda da ta gabata, hukumar ta gudanar da gangamin wayar da kai 76 da shirye-shiryen rediyo da talabijin 15, tare da ba mutane 87 masu amfani da miyagun kwayoyi shawara da jinya.

Har ila yau, ya bayyana cewa an kwato miyagun kwayoyi masu nauyin kilogram 6,337.517, yayin da wani mutum mai suna Osho Akindele ya samu daurin shekaru 20 a gidan yari saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi.

Kwamandan ya kuma bayyana cewa an kama wasu tsofaffi biyu masu shekaru 78 da 80 bisa zargin mallaka da safarar miyagun kwayoyi, yana kira ga al’umma da su hada kai da hukumomi wajen yaki da matsalar miyagun kwayoyi.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
Next Post: Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye

Karin Labarai Masu Alaka

An Kara Wa’adin Zaman Kurkuku A Senegal Ga Masu Auren Jinsi Afrika
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika
Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku Wasanni
  • Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba” Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.