Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

NSCIA Ta Gargadi Gwamnati Kan Zargin Tauye Haƙƙin Musulmi
Published: June 30, 2026 at 4:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Ƙolin Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (NSCIA) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki matakan gaggawa domin magance abin da ta bayyana a matsayin hare-haren nuna wariya da kuma tauye haƙƙin Musulmi a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Majalisar ta bayyana cewa idan ba a ɗauki matakan da suka dace ba cikin gaggawa, hakan na iya haifar da ƙarin damuwa da rashin gamsuwa a tsakanin al’ummar Musulmi.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na NSCIA, Abbas Jimoh, ya fitar a madadin majalisar, wadda ke ƙarƙashin jagorancin Sarkin Musulmi na Najeriya, Mai Alfarma Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar.

A cikin sanarwar, majalisar ta nuna damuwa kan abin da ta ce na ci gaba da faruwa na nuna wariya ga Musulmi da kuma tauye musu wasu haƙƙoƙi da kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanadar.

NSCIA ta jaddada cewa Najeriya ƙasa ce da ke bai wa kowane ɗan ƙasa damar gudanar da addininsa cikin walwala da ‘yanci, don haka ya zama wajibi gwamnati da hukumomin tsaro su tabbatar da kare waɗannan haƙƙoƙi ba tare da nuna bambanci ba.

Majalisar ta kuma yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da bincike kan duk wasu korafe-korafe da suka shafi tauye ‘yancin addini tare da ɗaukar matakan da suka dace domin tabbatar da adalci da zaman lafiya.

NSCIA ta ce tana sa ran gwamnati za ta yi abin da ya dace cikin gaggawa domin kare haɗin kai da zaman lafiya a ƙasa, tare da tabbatar da cewa an mutunta haƙƙin kowane ɗan ƙasa ba tare da la’akari da addininsa ko asalinsa ba.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: PDP Ta Koka Kan Rushe-rushe, Korar Gombawa Motors da Zaɓen Kananan Hukumomi A Gombe
Next Post: An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas

Karin Labarai Masu Alaka

An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji Najeriya
Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
  • Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
  • Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.