Ofishin Mai Bai wa Gwamnan jihar Bauchi Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Mukhtari Gidado, Jarman Alkaleri, ya shirya taron horaswa na kwanaki uku ga ‘yan jaridar Gidan Gwamnatin jihar Bauchi a jihar Gombe.
An gudanar da taron ne daga 1 zuwa 3 ga Yulin 2026 a Flourish Hotels Ltd., Gombe, inda aka mayar da hankali kan haɓaka ƙwarewar mahalarta a fannin fasahar sadarwar zamani da kuma ƙarfafa bin ƙa’idojin ɗa’a a aikin jarida.

Taron, mai taken “Ƙarfafa Ƙwarewar ‘Yan Jaridar Gidan Gwamnatin Jihar Bauchi ta Hanyar Horar da Su kan Fasahar Zamani da Kayan Aikin Jarida Masu Bin Ɗa’a domin Inganta Isar da Manufofin Gwamnati da Gina Amincewar Jama’a,” ya bai wa mahalarta ilimi da sabbin dabarun aikin jarida, waɗanda za su taimaka musu wajen isar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati cikin inganci tare da ƙarfafa amincewar al’umma.
A jawabin maraba, Mai Bai wa Gwamna Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Alhaji Mukhtari Gidado, ya jaddada aniyar Gwamnatin Jihar Bauchi na ci gaba da bunƙasa ƙwarewar ‘yan jarida ta hanyar shirya irin waɗannan tarukan horaswa akai-akai domin su dace da sauye-sauyen da ake samu a harkar yaɗa labarai.

Shi ma da yake jawabi a madadin Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Bauchi), Kwamishinan Yaɗa Labarai da Sadarwa na jihar, Dr. Usman Shehu Usman, ya taya mahalartan murnar samun damar halartar taron, tare da buƙatar su yi amfani da ilimin da suka samu wajen ƙara ƙwarewa da inganta ayyukansu.
A nasa jawabin, Mataimaki na Musamman kan Sadarwa ga Gwamnan jihar Bauchi, kuma fitaccen ɗan jarida Alhaji Abdulwahab Muhammad, ya bayyana taron a matsayin wanda ya zo a kan lokaci kuma mai matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa aikin yaɗa labaran gwamnati.
Ya kuma buƙaci mahalarta su yi amfani da ilimi da ƙwarewar da suka samu domin inganta ayyukansu da kuma tabbatar da ingantacciyar sadarwa tsakanin gwamnati da al’umma.

Haka kuma, taron ya bai wa mahalarta damar musayar ra’ayoyi, haɓaka ƙwarewarsu ta aiki, tare da tattauna sabbin hanyoyin amfani da fasahar zamani wajen inganta sadarwar gwamnati da jama’a.


