Gwamnatin jihar Yobe dake arewa maso Gabashin Najeriya ta sake jaddada aniyarta na rage yawan mutuwar yara masu ƙasa da shekara biyar ta hanyar ci gaba da aiwatar da shirin SARMAAN, tare da shirye-shiryen faɗaɗa shi zuwa dukkan ƙananan hukumomi 17 na jihar.
Ana gudanar da shirin ne na haɗin gwiwa da African Field Epidemiology Network (AFENET) Nigeria, inda aka faɗaɗa shi daga ƙananan hukumomi 10 a matakin farko zuwa 13 a zagayen da ake gudanarwa a halin yanzu.
Babban Jami’in Hulɗa da Gwamna kan Kula da Lafiya a Matakin Farko, Dakta Umar Ciroma, ya ce shirin ya samo asali ne daga shawarar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ga ƙasashen da ke fama da yawan mutuwar yara masu ƙasa da shekara biyar.
Ya bayyana cewa ana bai wa yara ƙwayar maganin Azithromycin sau shida cikin tsawon shekaru uku, ana ba su duk bayan watanni shida, domin kariya daga wasu cututtukan ƙwayoyin bacteria da ke haddasa ciwon huhu, cutar sepsis, cututtukan fata, trachoma da kuma wasu nau’ikan gudawa.
Al’ummomi da dama a faɗin jihar sun ci gaba da karɓar shirin hannu bibbiyu, inda iyaye da masu kula da yara suka bayyana cewa sun lura da ingantuwar lafiyar yaransu bayan karɓar maganin.
Haka kuma, Cibiyar Binciken Lafiya ta Najeriya (NIMR) na sa ido tare da tantance tasirin shirin wajen tabbatar da cewa duk wani mataki na gaba zai kasance bisa hujjojin kimiyya.
Masu ruwa da tsaki sun ce haɗin gwiwar gwamnati, ma’aikatan lafiya, abokan hulɗar ci gaba da al’ummomi na ƙara wa jama’a kwarin gwiwa kan shirin, tare da ƙarfafa ƙoƙarin rage mutuwar yara da za a iya kauce wa a jihar Yobe.


