Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
Published: July 8, 2026 at 8:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Jigawa ta sake tabbatar da aniyarta na ci gaba da tallafa wa Cibiyar Bunƙasa Fasaha (Technology Incubation Centre – TIC) da ke Dutse domin bunƙasa kasuwancin fasaha, haɓaka harkokin kasuwanci da samar da ayyukan yi a faɗin jihar.

Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi Manajan Cibiyar, Injiniya Shukuranu Uzairu, tare da tawagarsa a ziyarar girmamawa da suka kai masa a ofishinsa.

Dagaceri ya bayyana TIC Dutse a matsayin cibiyar da ta yi fice a jihar, inda ya yaba da irin gudunmawar da take bayarwa wajen bunƙasa ƙirƙire-ƙirƙire da tallafa wa masu sana’o’i da ‘yan kasuwa.

Ya ce gwamnatin jihar tana sane da irin ayyukan alheri da cibiyar ke yi wajen haɓaka sabbin dabarun kasuwanci, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da haɗa kai da ita domin ƙara faɗaɗa tasirinta wajen bunƙasa tattalin arziki.

Tun da farko, Manajan Cibiyar, Injiniya Shukuranu Uzairu, ya ce ziyarar na daga cikin shirin ƙarfafa alaƙa da masu ruwa da tsaki da kuma gano sabbin hanyoyin haɗin gwiwa tun bayan da ya karɓi ragamar jagorancin cibiyar.

Ya bayyana cewa shirin Cibiyoyin Bunƙasa Fasaha ya taka muhimmiyar rawa wajen haɓaka ƙirƙire-ƙirƙire da kasuwanci, yana mai cewa tallafin gwamnati ga irin waɗannan cibiyoyi a faɗin ƙasar ya taimaka wajen kafa dubban ƙanana da matsakaitan masana’antu (SMEs), tare da samar da ayyukan yi kai tsaye da kuma a kaikaice.

Uzairu ya roƙi gwamnatin jihar da ta ƙara tallafa wa cibiyar ta hanyar bunƙasa kayayyakin more rayuwa, samar da wuraren masana’antu ga waɗanda suka kammala shirin koyon sana’a da matasa masu tasowa a harkokin kasuwanci, da kuma ƙarfafa sauran shirye-shiryen haɗin gwiwa domin faɗaɗa ayyukan cibiyar.

Ziyarar ta nuna ƙudirin Gwamnatin jihar Jigawa na amfani da fasaha, ƙirƙire-ƙirƙire da bunƙasa harkokin kasuwanci a matsayin hanyoyin inganta tattalin arziki da samar da ayyukan yi ga matasa.

Afrika, Kimiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
Next Post: Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika
  • Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.