Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kano: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Amince da Garo A Matsayin Mataimakinsa Na 2027
Published: July 15, 2026 at 5:25 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanar da sake tsayar da Mataimakin Gwamna, Alhaji Murtala Sule Galadima Garo, a matsayin abokin takararsa domin zaɓen gwamnan jihar na shekarar 2027.

Sanarwar ta fito ne cikin wata takarda da Darakta Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gidan Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Litinin.

Gwamna Yusuf ya bayyana matakin ne yayin wani taron dabarun siyasa da ya yi da masu riƙe da muƙaman gwamnatin tarayya daga jihar Kano da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa, wanda aka gudanar a masaukin gwamnatin jihar da ke Abuja.

Ya ce ya yanke shawarar sake zaɓen Murtala Garo ne bisa irin biyayya, jajircewa da ƙwazon da ya nuna wajen gudanar da aikinsa tun bayan hawansu mulki.

Gwamnan ya ce ya gamsu da yadda suke aiki tare, yana mai bayyana Mataimakin Gwamnan a matsayin mutum mai ƙwarewa, sadaukarwa da cikakken ɗaukar nauyin da ya rataya a wuyansa.

A cewarsa, “Ban taɓa nadamar zaɓen Garo a matsayin Mataimakina ba. Ya tabbatar da cewa shi ne ya dace da wannan matsayi, kuma ina da cikakken yaƙini da ƙwarewarsa.”

Gwamna Yusuf ya kuma bayyana cikakken goyon bayansa ga Mataimakin Gwamnan, yana mai cewa gudummawar da yake bayarwa ta ƙara ƙarfafa ƙoƙarin gwamnatin jihar na samar da ci gaba mai ma’ana ga al’ummar Kano.

Ya yi kira ga shugabannin jam’iyya, masu riƙe da muƙaman siyasa da magoya baya da su ci gaba da haɗa kai tare da mara wa gwamnati baya yayin da take ci gaba da aiwatar da manufofinta tare da shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Shirye-Shirye, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye
Next Post: Bayan Rikicin Manoma Da Makiyaya, Kwamitin White Paper Ya Ziyarci Bojude Da Kwami

Karin Labarai Masu Alaka

Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
  • Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.