Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanar da sake tsayar da Mataimakin Gwamna, Alhaji Murtala Sule Galadima Garo, a matsayin abokin takararsa domin zaɓen gwamnan jihar na shekarar 2027.
Sanarwar ta fito ne cikin wata takarda da Darakta Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gidan Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Litinin.
Gwamna Yusuf ya bayyana matakin ne yayin wani taron dabarun siyasa da ya yi da masu riƙe da muƙaman gwamnatin tarayya daga jihar Kano da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa, wanda aka gudanar a masaukin gwamnatin jihar da ke Abuja.
Ya ce ya yanke shawarar sake zaɓen Murtala Garo ne bisa irin biyayya, jajircewa da ƙwazon da ya nuna wajen gudanar da aikinsa tun bayan hawansu mulki.
Gwamnan ya ce ya gamsu da yadda suke aiki tare, yana mai bayyana Mataimakin Gwamnan a matsayin mutum mai ƙwarewa, sadaukarwa da cikakken ɗaukar nauyin da ya rataya a wuyansa.
A cewarsa, “Ban taɓa nadamar zaɓen Garo a matsayin Mataimakina ba. Ya tabbatar da cewa shi ne ya dace da wannan matsayi, kuma ina da cikakken yaƙini da ƙwarewarsa.”
Gwamna Yusuf ya kuma bayyana cikakken goyon bayansa ga Mataimakin Gwamnan, yana mai cewa gudummawar da yake bayarwa ta ƙara ƙarfafa ƙoƙarin gwamnatin jihar na samar da ci gaba mai ma’ana ga al’ummar Kano.
Ya yi kira ga shugabannin jam’iyya, masu riƙe da muƙaman siyasa da magoya baya da su ci gaba da haɗa kai tare da mara wa gwamnati baya yayin da take ci gaba da aiwatar da manufofinta tare da shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.


