Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
Published: July 25, 2026 at 4:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda da dama tare da tarwatsa maboyarsu a wasu sabbin hare-hare da suka kai ta sama da ƙasa a jihohin Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma.

Hare-haren da aka gudanar ƙarƙashin Operation HADIN KAI da Operation FANSAN YAMMA sun kuma haifar da ceto waɗanda aka sace, kama masu garkuwa da mutane da kuma ƙwato makamai da sauran kayayyakin sadarwa.

A Jihar Borno, dakarun Bataliya ta 212 sun kama wani da ake zargin ɗan ƙungiyar ISWAP ne a kan hanyar Maiduguri zuwa Monguno, inda aka same shi da na’urar Starlink, na’urar Wi-Fi mai tashoshi shida, wayar salula da kuɗi.

Haka kuma, dakarun Bataliya ta 82 sun ceto wasu ‘yan mata biyu a yankin Gwoza, waɗanda suka bayyana cewa an sace su tun watan Agustan 2025 a kan hanyar Pulka zuwa Ngoshe, kuma suka tsere daga sansanin ‘yan ta’adda da ke Dutsen hMandara.

A Jihar Yobe kuwa, dakarun Brigade ta 27 sun daƙile wani harin dare da ‘yan ta’adda suka kai wani wurin binciken sojoji a hanyar Buni Yadi zuwa Buni Gari da ke ƙaramar hukumar Gujba. Sai dai sojoji biyu sun rasa rayukansu yayin fafatawar, yayin da aka lalata motar yaƙi ta ‘yan ta’addan.

A wani samame kuma, dakarun Bataliya ta 233 tare da haɗin gwiwar mafarauta sun kama mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a ƙauyen Jegalari na ƙaramar hukumar Fune, inda aka ƙwato bindigogi, alburusai da wayoyin hannu.

Rahoton ya ce hare-haren sama da aka kai bisa bayanan sirri sun yi mummunar illa ga ‘yan ta’adda. A yankin Kala Balia da ke ƙaramar hukumar Marte ta Borno, jiragen yaƙin sama sun kashe kusan ‘yan ta’adda 15 bayan an gano maboyarsu.

Haka kuma, a wani harin dare da aka kai tsakanin Bama da Maiduguri, an kashe wasu ‘yan ta’adda takwas bayan jiragen yaƙi sun yi luguden wuta kan wuraren da aka gano motsinsu.

A Arewa maso Yamma, dakarun Operation FANSAN YAMMA sun fafata da ‘yan ta’adda a Dutsen Gambada da ke ƙaramar hukumar Gummi ta Jihar Zamfara.

Haka kuma, dakarun Brigade ta 12 sun hana wani yunƙurin satar mutane a kan hanyar Kabba zuwa Ayere a Jihar Kogi tare da ceto mutum shida da aka sace, waɗanda aka kai Asibitin St. Joseph da ke Kabba domin kula da lafiyarsu. A Jihar Nasarawa ma, dakarun Operation WHIRL STROKE sun ceto wani da aka yi garkuwa da shi a yankin Tunga na ƙaramar hukumar Awe.

A Kudu maso Gabas kuwa, dakarun Operation UDO KA sun kai samame wani maboyar masu aikata laifuka a yankin Awara Waterside, inda suka ƙwato bindigogin Lee-Enfield da G3 tare da alburusai masu yawa. Rundunar Sojin Najeriya ta ce waɗannan nasarori sun nuna cewa ana ci gaba da matsa wa ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane lamba ta hanyar amfani da ingantattun bayanan sirri da haɗin gwiwar hare-haren sama da ƙasa, tare da jaddada aniyarta na ci gaba da yaƙi har sai an kawar da dukkan ƙungiyoyin masu aikata laifuka a faɗin ƙasar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
Next Post: NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis

Karin Labarai Masu Alaka

Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda Afrika
Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
Dr. Zainab Gwamna Ta Hada Mata Fiye Da 6,000 Domin Haɗin Kai Da Ci Gaba A Gombe Najeriya
Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
  • Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
  • Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP Afrika
  • Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
  • Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya
  • Arsenal Tana Ci Gaba Da Kokarin Dauko Morgan Rogers Wasanni
  • Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna Amurka
  • Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.