Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi
Published: November 30, 2025 at 7:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Zamu tabbatar da kawo karshen hadura a lokacin Bukukuwan karshen shekara – inji Jami’an Hukumar kiyaye hadura a Gombe.

Hukumar kiyaye hadura ta kasa reshen jihar Gombe ta shirya taron fadakar da jama’a game da illar gudu fiye da kima, tare da tukin ganganci yayin bukukuwan karshen shekara.

Kwamandan hukumar kiyaye hadura a jihar Gombe, Mr Samson Kaura ne ya bayyana haka lokacin jawabi ga direbobi da sauran jama’a, yayin gangamin a dakin taro na tashar Dankwanbo Mega Park dake Gombe.

Mr. Kaura, ya tabbatar da cewa ana samun yawan tafiye tafiye a karshen shekara, a saboda haka yabukaci masu ababen hawa da su rika lura tare da bin ka’idojin hanya domin kare rayuwar al’umma.

Ya tabbatar da cewa, ansamu hadura fiye da arba’in da shida a tsakiyar wannan shekarar, kuma mutane sha bakwai sun mutu a jihar Gombe.

A jawaban su, shugaban riko na tashar Dankwanbo Mega Park Malam Sani Sabo da shugaban kungiyar ‘yan achaba a jihar Gombe, Malam Kabiru Jafaru sun bukaci gwamnati da tayi la’akari da gyara hanyoyi da suka lalace a jihar domin gujewa samun hadura.

Malam Sani Sabo da Kabiru Jafaru, sun lissafo hanyar Gombe zuwa Dukku zuwa Darazo, hanyar Gombe zuwa Biu zuwa Maiduguri da hanyar Gombe zuwa Bauchi a matsayin hanyoyi masu muni. Wanda kuma suna haifar da hadura saboda lalacewar su, Inda su kayi fatan gwamnati zata kawo karshen wannan wahalhalu da jama’a ke fuskanta.

A nasu bangaren, daraktar hukumar wayar da kan al’umma jihar Gombe Miss Adalin Waye Patari, shugaban Direbobi na NURTW Malam Musa Yunusa da hakimin Kagarawal Alhaji Usman Ali sun bukaci Direbobi dasu gujewa shaye-shaye a yayin tuki, tare da yawaita gudu fiye da kima.

Inda suka tabbatar da cigaba da fadakar da mambobin su da jama’ar gari domin gujewa samun hadura a fadin kasar nan.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Next Post: Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
  • Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
  • Hawan Sallah Daga Masarautar Misau Afrika
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
  • Harin Ukraine Yayi Mummunan Barna A Rasha Afrika
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.