Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

FIFA Ta Buɗe Bincike Kan Koci Hossam Hassan Na Masar
Published: August 21, 2026 at 6:26 PM | By: Bala Hassan

FIFA TA BUƊE BINCIKEN LADABTARWA KAN KOCI HOSSAM HASSAN NA MASAR

Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya, FIFA, ta buɗe binciken ladabtarwa kan kocin tawagar ƙasar Masar, Hossam Hassan, bayan wasan da Masar ta fafata da Argentina a gasar cin Kofin Duniya ta FIFA ta 2026.

Ana binciken Hassan ne kan wasu kalamai da ya yi kafin da kuma bayan wasan, inda FIFA ke duba ko kalaman sun saɓa wa dokokin ladabtarwa na hukumar.

Daga cikin abubuwan da ake bincike akwai goyon bayan da Hassan ya nuna a bainar jama’a ga Falasɗinu, da kuma zargin da ya yi cewa an fifita Argentina saboda matsayin Lionel Messi, abubuwan kasuwanci da kuma kasancewar Argentina zakarar duniya.

Kocin na Masar ya kuma yi zargin cewa an yi wa tawagarsa rashin adalci da gangan a yayin gasar, yana mai cewa wasu abubuwan da suka shafi wasan sun samo asali ne daga dalilai na waje da na cikin gida.

Rahotanni sun ce Hassan ya ƙara da cewa **“babu adalci”** a gasar, tare da tambayar ko an gudanar da wasan ne bisa ƙa’idojin FIFA na adalci da girmama juna.

FIFA ta sanya takardar shari’ar ladabtarwar da kuma rahoton binciken a cikin Legal Portal na hukumar, yayin da yanzu ake jiran hukuncin kwamitin ladabtarwar.

Sakamakon binciken zai iya bayyana ko Hossam Hassan zai fuskanci wani hukunci ko takunkumi sakamakon kalaman da ya yi dangane da wasan Argentina da Masar.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Maulidi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Hutu
Next Post: Arsenal Ta Fara Kare Kambun Gasar Premier League Da Ci 3-0 A Kan Coventry City

Karin Labarai Masu Alaka

Chukwueze, Ya Ci Gaba Da Riƙe Rigarsa Mai Lamba 21 A AC Milan Wasanni
Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Arsenal Tana Ci Gaba Da Kokarin Dauko Morgan Rogers Wasanni
Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
Galatasaray Ta Yi Watsi Da Tayin €150m Daga Al-Hilal Kan Victor Osimhen Wasanni
Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.