Galatasaray Ta Yi Watsi da Tayin €150m Daga Al-Hilal Kan Victor Osimhen
Kungiyar Galatasaray ta Turkiyya ta yi watsi da tayin da ya kai Yuro miliyan 150 daga Al-Hilal ta Saudiyya domin daukar dan wasan gaba na Super Eagles, Victor Osimhen.
A cewar rahoton BSN Sports, Al-Hilal ta nuna sha’awarta ta daukar Osimhen, wanda Galatasaray ta dauka daga Napoli a farkon kakar wasan da ta gabata.
Rahoton ya ce tawagar Saudiyya karkashin jagorancin Yarima Nawaf bin Saad ta fara da tayin baki na Yuro miliyan 130, inda yariman ya sanar da shugabannin Galatasaray cewa zai zo Istanbul da kansa idan tattaunawar ta zama ta hukuma.
Bayan haka, Al-Hilal ta yi wa Osimhen tayin albashin Yuro miliyan 50 a duk shekara, amma Galatasaray ta sanar da kungiyar Saudiyyar cewa ba ta da niyyar sayar da dan wasan.
Daga bisani Al-Hilal ta kara tayin zuwa Yuro miliyan 150, amma har yanzu shugaban Galatasaray, Dursun Özbek, da shugabannin kungiyar sun yi fatali da tayin, tare da bayyana aniyarsu ta ci gaba da rike dan wasan.
Osimhen, wanda rahoton ya ce yana matukar farin ciki a Galatasaray, ya kuma bayyana cewa abin da ya fi mayar da hankali a kai shi ne kakar wasa ta gaba, ba batun kudi ba.
Dan wasan na Najeriya ya kuma fara kakar gasar lig din Turkiyya da kyau, bayan ya zura kwallaye biyu a wasan makon farko da Çorum FK.


