Wani fitaccen malamin addinin Kirista daga jihar Kaduna, Fasto Dr. Yohanna Buru, wanda ya yi fice wajen inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai, ya shiga cikin dubban Musulmi domin bikin Maulidin Annabi Muhammad (SAW) a jihar Kaduna.
Fasto Buru, wanda shi ne Babban Fasto na Christ Evangelical and Life Intervention Ministry, ya ce wannan shi ne karo na 11 a jere da yake halartar bukukuwan Mauludi tare da Musulmi a Kaduna da sauran sassan Arewacin Najeriya.
Faston ya halarci bikin ne tare da wasu shugabannin Kiristoci, ciki har da Fasto George John, Rabaran Rawland Sanda da Gabriel Stephen, inda suka shiga cikin dubban Musulmi da suka taru a filin Murtala Mohammed Square da ke Kaduna domin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW).
Da yake jawabi a wajen taron, Fasto Buru ya ce halartar Mauludi da yake yi na daga cikin kokarinsa na inganta zaman lafiya, hakuri da juna, mutunta addinai da kuma karfafa kyakkyawar alaka tsakanin Kiristoci da Musulmi.
Ya ce bukukuwan Mauludi na samar da wata dama ta musamman da mabiya addinai daban-daban za su hadu, su tattauna tare da kara fahimtar juna, yana mai cewa zaman lafiya na bukatar tattaunawa, hakuri da kuma mutunta juna.
A cikin wata lacca kan zaman lafiya da hadin kai, Fasto Buru ya bayyana Annabi Muhammad (SAW) a matsayin Manzo wanda koyarwarsa kan zaman lafiya, soyayya da tausayi ta shafi daukacin bil’adama.
Ya ce, “Annabi Muhammad (SAW) Manzo ne ga dukkan bil’adama, ba tare da la’akari da kabila, al’ada, yanki, launi, jinsi ko kasa ba.”
Fasto Buru ya yi kira ga ‘yan Najeriya daga kabilu da addinai daban-daban da su rungumi juna, su yafe wa juna kura-kuran baya, sannan su hada kai wajen gina kasa mai zaman lafiya da hadin kai.
Ya ce Kiristoci da Musulmi sun yi imani da Ubangiji guda, don haka ya kamata su yi amfani da Littafi Mai Tsarki da Al-Qur’ani wajen samun jagoranci kan yadda za a tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna.
Faston ya kuma bayyana cewa halartar bukukuwan Mauludi da yake yi ba ya nufin ya yi watsi da addininsa na Kirista, yana mai cewa yin hakan wani bangare ne na kokarinsa na karfafa fahimtar juna tsakanin mabiya addinai.
Ya bayyana cewa a kowace shekara yana halartar bukukuwan Mauludi sama da 30 a jihohin Najeriya daban-daban da kuma wasu kasashen makwabta, domin yin murnar tare da Musulmi da kuma yada sakon zaman lafiya, hadin kai da hakurin addini.
Ya ce, “A kowace shekara ina halartar bukukuwan Mauludi sama da 30 daga jiha zuwa jiha, har ma da wasu kasashe makwabta, da nufin yin murnar tare da Musulmi da kuma inganta zaman lafiya, hadin kai da hakurin addini.”
Fasto Buru ya bukaci Kiristoci da Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci na Mauludi wajen yada soyayya, yafiya, hadin kai da zaman lafiya a fadin Najeriya.
Shi ma da yake jawabi, Rabaran Rawland Sanda ya ce shugabannin Kiristoci na ci gaba da amsa gayyatar Musulmi domin halartar bukukuwan Mauludi, a matsayin wata hanya ta karfafa alaka da fahimtar juna tsakanin mabiya addinan biyu.
Ya ce, “A kowace shekara Musulmi kan gayyace mu zuwa bukukuwan Mauludi, kuma kullum muna zuwa domin yin murna tare da su, saboda mun yi imani da inganta zaman lafiya, hadin kai da kyakkyawar alaka tsakanin mutane masu addinai daban-daban.”
Ya kara da cewa Kiristoci ma suna gayyatar Musulmi zuwa majami’u a lokacin bikin Kirsimeti domin tunawa da haihuwar Yesu Almasihu.
Ya ce, “Muna taya Musulmi a fadin duniya murna, tare da addu’ar samun zaman lafiya da hadin kai a kasarmu.”
Shi ma wani malamin addinin Musulunci, Imam Mohammed Musa, tare da Imam Iliyasu Yusuf na Zariya, Kaduna, sun yabawa Fasto Buru da sauran shugabannin Kiristoci bisa halartar bikin Mauludi tare da Musulmi.
Malaman sun bayyana wannan al’ada a matsayin wata muhimmiyar hanya da ke karfafa fahimtar juna, mutunta juna da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai daban-daban.
Sun ce tsawon shekaru 11, Fasto Dr. Yohanna Buru ya kasance yana halartar bukukuwan Mauludi tare da Musulmi a Kaduna da sauran sassan Arewacin Najeriya, lamarin da suka ce ya zama muhimmiyar hanya wajen hada kan mabiya addinai daban-daban.
Malaman sun kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta yi la’akari da bai wa Fasto Buru lambar yabo ta kasa, bisa irin gudunmawar da yake bayarwa wajen inganta zaman lafiya, hakurin addini da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai a Najeriya.


