Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabashin Najeriya (NEDC) ta musanta wani sako da ke yawo game da wani tallafin karatu na digirin MSc, inda ta bayyana bayanan a matsayin na bogi kuma ba tare da izinin hukumar ba.
A cikin wata sanarwa, hukumar ta ce a halin yanzu ba ta karbar neman tallafin karatun MSc da aka bayyana a cikin sakon da ke yawo ba. Sakon ya kuma kunshi wasu sharudda tare da umartar masu neman tallafin da su kai takardunsu ofishin NEDC da ke Polo, Maiduguri.
NEDC ta bukaci jama’a, musamman masu neman tallafin da sauran masu ruwa da tsaki, da su yi watsi da wannan bayanin, tare da kaucewa mika takardun sirri ga wasu mutane ko wuraren da ke ikirarin suna wakiltar hukumar wajen gudanar da wannan shirin.
Hukumar ta yi gargadin musamman kan mika takardu kamar NIN, takardar admission, katin shaida da takardar shedar zama dan asalin wata jiha (Indigene Certificate) ga mutanen da ba su da izini.
NEDC ta kuma bukaci jama’a da su kasance cikin taka-tsan-tsan domin kauce wa fadawa cikin shirye-shiryen damfara da kuma amfani da sunan hukumar ba tare da izini ba.
Hukumar ta shawarci jama’ar da ke son samun sahihan bayanai kan shirye-shiryenta, ayyukan tallafi da sauran damarmaki da su rika dogaro da hanyoyin sadarwa na hukuma na NEDC da kuma sanarwar da hukumar ta tabbatar.


