Ministan Tsaron Najeriya, Alh. Mohammed Badaru Abubakar, ya yi murabus daga mukaminsa yau Litinin
A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 1 ga Disamba, wadda ya aika wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Badaru Abubakar ya bayyana cewa ya ɗauki wannan mataki ne saboda yanayin rashin lafiya.
Shugaba Tinubu ya amince da murabus ɗin tare da gode masa bisa hidimar da ya yi wa ƙasa a lokacin da yake rike da mukamin.
Alhaji Mohammed Badaru Abubakar yayi wa’adi biyu a kan kujerar gwamnan Jihar Jigawa daga 2015 zuwa 2023. Shugaba Tinubu ya bada shi ministan tsaro a watan Agusta na 2023. Ana sa ran cewa watakila nan gaba a cikin wannan makon shugaba Tinubu zai sanar da majalisar dattijai a kan wanda zai gaji kujerar ministan tsaron.


