Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran
Published: March 1, 2026 at 5:01 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka da Isra’ila sun kai hari kan Iran yau Asabar, inda suka auna manyan shugabannnin kasar, suna masu kiran da a kifar da gwamnatin kasar, ita kuma Iran ta maida martani tare da harba makamai masu linzami kan Isra’ila da kasashe makwabta.

Shugaba Donald Trump, a mataki da ake kallo a zaman kasada mafi girma a manufofin harkokin wajen gwamnatinsa, ya kaddamarda yaki kan kasar da Amurka take kallo a zaman makiyarta na shekaru masu yawan gaske, yace harin ta kai shine da nufin kawar da barazana, da kuma tabbatar da ganin Iran bata habaka makaman Nukiliya ba.

Yayi kira ga jami’an tsaron kasar su ajiye makaman su, daga nan ya gayyaci al’umar kasar su kifar da gwamnatin kasar da zarar an kawo karshen hare hare da ake kaiwa kan kasar.

Tehran ta kira harin da aka fara da safiyar ranar asabar kuma ya auna sassa daban daban na kasar, da cewa hari da aka kai mata ba tare da takala ba, kuma baya bisa doka.

Tashar talabijin ta kasar da ake kira -Al-Alam, tace shugaban addinin kasar Ali Khameni, wadda ba’a ji daga gareshi ba zuwa yanzu, zai yi jawabi nan ba da jumawa ba.

A birane a duk fadin kasar, karar fashe fashe sun janyo tsoro. Mazauna biranen suna gaggawar kwaso yara daga Makaranta, da gudu daga wurare da suke zaton za’a kai wa hari.

Isra’ila ta hana jama’a yin tarurruka, ta rufe makarantu da masana’antu, kuma ta kawashe maras lafiya a asibitoci zuwa wurare dake karkashin kasa, a dai dai lokacin da Iran ta harba makamai masu linzami da ta auna kan Isra’ila, a zaman martanin harin da Amurka da Isra’ila suka kai mata.

Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ayyana dokar ta baci a duk fadin kasar, ya gargadi jama’a dangane da hare hare da Iran zata kai mata da makamai masu linzami da jirage da basu da matuka.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran
Next Post: Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika
Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
  • An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
  • Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
  • Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
  • Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.