Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
Published: January 15, 2026 at 4:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka ta fara janye wasu ma’aikata daga sansanonin sojanta a yankin gabas ta tsakiya, a bayan da wani babban jami’in Iran ya gargadi makwabtansu cewa Iran zata kai hari kan sansanonin Amurka idan har aka kai mata hari.

A yayin da hukumomi a birnin Teheran ke kokarin kwantar da wutar tarzoma mafi muni tun bayan juyin juya halin Islama da aka yi, Teheran tana son yin hannunka mai sanda ma shugaba Donald Trump da barazanarsa ta tsoma baki domin goyon bayan masu zanga zangar kin jinin gwamnati.

Wani jami’in Amurka da bai so a fadi sunansa ba yace Amurka tana kwashe ma’aikata daga wasu muhimman sansanoninta a saboda karuwar tankiya.

Wani jami’in soja a kasar yammaci yace a bisa dukkan alamu Amurka ta yanke shawarar zata kai ma kasar Iran farmaki, amma kuma yace irin wannan dabi’a gwamnatin Trump ta saba nunawa na haddasa yanayin kokwanto a kan zata kai ne ko ba zata kai harin ba.

Amma kuma a fadarsa ta White House, shugaba Trump ya nuna alamun kamar yana jira ya ga yadda lamarin zai wakana ne, trump yace wata majiya mai tushe ta fada masa cewa yawan kashe kashe ya ragu, kuma babu wani shirin da aka yi a yanzu na zartas da hukumcin kisa a kan mutane masu yawa.

Wasu jami’an Turai guda biyu ma sun ce watakila nan da sa’o’i 24 Amurka zata kai hari a kan kasar Iran haka ma wani jami’in gwamnatin bani Isra’ila yace da ala mun shugaba Trump ya yanke shawarar zai tsoma hannu a Iran, amma ba a san irin farmakin da zai kai ko kuma lokacin kaiwa ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland
Next Post: Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka Amurka
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka
  • Hukumar ICPC Ta Kwato Makudan Kudade Rediyo
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.