Amurka ta hambare gwanatin shugaba Maduro a Venezuela, kuma tace zata gudanar da harkokin kasar har zuwa lokacin da ya dace. Shugaban Amurka Donald Trump ne ya bayyana haka a wani taron da manema labarai a Mar-Largo, wurin shakatawarsa dake jihar Florida.
Da manema labarai suka matsa neman karin bayani kan yadda Amurka zata tafiyar da harkokin kasar ta Venezuela, shugaba Trump bai bada amsa kai tsaye ba. Yace “zamu tafiyarda harkokin kasar da gungun mutane. Kuma zamu tabbatar da cewa an tafiyar da kasar yadda ya kamata.” inji shugaban na Amurka.
Da ‘yan jarida suka matsa don jin yadda za’a aiwatar da shirin, shugaba Trump, yace “ana yin haka a halin yanzu.” Muna zabar mutane. Muna magana da mutane. Kuma za mu sanar da ku ko su wanene wadan nan mutanne, inji shugaba Trump.
Da yake magana a taron na manema labarai, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, yace, Maduro ba shine halataccen shugaban Venezuela ba. Domin tun a shekara ta 2020 zamanin gwamnatin Trump ta farko Amurka ta tuhumi Maduro, haka itama gwamnatin Biden da kuma gwamnatiin Trump ta yanzu.
A taro da manema labaran, shugaba Trump ya gargadi shugaban kasar Columbia cewa ya shiga taitayinsa. Yana zarginsa da sarrafawa da safarar miyagun kwayoyi, Da aka tambayeshi gameda kasar Cuba, shugaba Trump, yace akwai bukatar ita ma Cuba a dubi lamarinta domin tana bukatar taimako.
Da suke maida martani kan wannan mataki, wakkilan majalisar dokokin Amurka ‘yan jam’iyyar Democrat, sunce jami’an gwamnati Trump basu gaya musu gaskiya ba a ganawarda suka yi da su a baya bayan nan gameda Venezuela, suko jami’an bangaren zartaswa sun fada musu basu da burin sauya gwamnati a Venezuela.


