Gwamna Inuwa Yahaya Ya Taya Kiristoci Murna; Ya Buƙaci Su Ci Gaba Da Addu’o’in Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Jihar Gombe Da Najeriya.
Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Kirista na jihar Gombe dama duniya baki ɗaya murnar bikin Kirsimeti na bana, inda ya bayyana bikin a matsayin lokacin dake karfafa ɗabi’un kauna, zaman lafiya, sadaukarwa da kuma haƙuri.

A saƙonsa na barka da Kirsimeti, Gwamnan yace bikin haihuwar Yesu Almasihu yana nuna muhimmin lokaci na yin nazari kan kyawawan halaye dake haɗa kan ƴan adam, ba tare da la’akari da addini ko asalinsu ba, sannan ya yi ƙira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da ririta zaman lafiyan da suke yi da juna tare.
Gwamna Inuwa Yahaya yace jihar Gombe ta kasance misali mai kyau na jituwa tsakanin addinai daban-daban, inda mutane masu bambancin addini da ƙabilu ke zaune tare kuma suna aiki tare cikin girmamawa da fahimtar juna.
“Wannan lokacin biki yana tunatar da mu ikon ƙauna, tausayi da sadaukarwa waɗanda kyawawan halaye ne da ke da mahimmanci ga koyarwar Yesu Almasihu.”
“Waɗannan ɗabi’u suna da matuƙar muhimmanci wajen wanzar da zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna a jiharmu da kuma ƙasa baki ɗaya,” in ji Gwamnan.
Gwamna Inuwa Yahaya, wanda kuma shine Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewa, ya yi ƙira ga Kiristoci su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwan wajen yin addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai, kwanciyar hankali da wadata a faɗin jihar da Najeriya, musamman a wannan lokacin da ake buƙatar juriya da haɗin kai don shawo kan ƙalubalen tattalin arziki, tsaro da zamantakewa.
Ya kuma yi ƙira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da jajircewa wajen tallafawa kokarin gwamnati na inganta walwalar jama’a.
Gwamnan ya tabbatarwa al’ummar Kiristan jajircewar gwamnatinsa na yancin yin addini, tabbatar da daidaito da kuma haɗa kan jama’a, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa zata ci gaba da damawa da duk al’ummar jihar a harkokin ci gaban da ake samu a jihar Gombe.
Ya kuma bayyana al’adar gwamnatin na bada tallafi ga kungiyoyin addini a lokutan bukukuwa don rage musu ɗawainiya, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin haɓaka haɗin kai da farin ciki tare.
Ya yi wa Kiristocin jihar Gombe da kewaye fatan alheri, farin ciki da cikar buri a bikin na Kirsimeti, yayin da ya yi ƙira ga duk ‘yan Najeriya su ƙara sadaukar da kansu ga haɗin kai, ‘yan’uwantaka da kuma zaman lafiya don ci gaban jihar da ƙasa baki ɗaya.


