An sace sama da masu ibada 20 a harin da aka kai cocin ECWA a Jihar Kogi
Akalla masu ibada 20 aka yi garkuwa da su bayan ’yan bindiga sun kai hari Cocin First ECWA da ke Ayetoro Kiri, Ƙaramar Hukumar Kabba/Bunu ta Jihar Kogi, yayin ibada a ranar Lahadi.
Rahotanni sun ce maharan sun shigo cocin ne suna harbe-harbe domin tayar da hankula, inda suka sace wasu daga cikin masu ibada sannan suka tsere tdazuzzuka, Mutum ɗaya mai suna JayJay ya mutu a harin.
Harin ya ƙara tayar da hankula kan tabarbarewar tsaro a yankin Okun, musamman ganin cewa wannan shi ne hari na biyu da aka kai wa coci cikin ’yan makonni, lamarin da ya sa mazauna yankin ke kira da a ƙara tsaurara matakan tsaro.


