Ana ci gaba da gwabza yaki, tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kai wa kasar Iran hari, inda suka kashe shugaban ta Ayatollah Ali Khameni. Isra’ila na ci gaba da kai hari Tehran, babban birnin Iran da kuma Beirut, babban birnin Lebanon, inda itama Iran ta mai da martani wajen kai hare-hare sansanonin sojin Amurka dake gabas ta tsakiya, ta kuma rufe mashigin ruwa na Hormuz, inda jiragen dakon man fetur ke ratsawa.
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da yiwuwar sojin Amurka cewa zasu yiwa jiragen dakon man fetur dafifi don su samu wucewa ta hanyar mashigin ruwa na Hormuz. Ita kuma Iran ta dau alwashin harbo duk wani jirgi da ya wuce ta nan.
Kasuwannin hada-hadar hannun jari sun rikice, yayin da farashin danyen man fetur ya tashi sakamakon yakin.
A jiya Talata ne kuma aka samu sabanin ra’ayi game da dalilin da ya sa Amurka ta kaiwa Iran hari tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da kuma sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio.
Trump ya ce ya umurci Isra’ila da ta kaiwa Iran hari saboda yana da yakinin Iran na da niyyar fara kawo musu hari. A nasa bangaren shi kuma Marco Rubio ya sha banban, inda ya shaidawa manema labarai ranar Litinin cewa Amurka ta kaiwa Iran hari ne saboda fargabar da ake yi na cewa Iran zata mai da martani game da shirin kaiwa Tehran hari da Isra’ila ta yi.
Ya ce mun san Isra’ila zata kai hari, kuma mun san cewa za’a mai da martani ta kai hari kan sojin Amurka, mun san idan bamu far musu ba zasu yi mana barna me yawa.


