Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran
Published: March 4, 2026 at 2:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ana ci gaba da gwabza yaki, tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kai wa kasar Iran hari, inda suka kashe shugaban ta Ayatollah Ali Khameni. Isra’ila na ci gaba da kai hari Tehran, babban birnin Iran da kuma Beirut, babban birnin Lebanon, inda itama Iran ta mai da martani wajen kai hare-hare sansanonin sojin Amurka dake gabas ta tsakiya, ta kuma rufe mashigin ruwa na Hormuz, inda jiragen dakon man fetur ke ratsawa.

Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da yiwuwar sojin Amurka cewa zasu yiwa jiragen dakon man fetur dafifi don su samu wucewa ta hanyar mashigin ruwa na Hormuz. Ita kuma Iran ta dau alwashin harbo duk wani jirgi da ya wuce ta nan.

Kasuwannin hada-hadar hannun jari sun rikice, yayin da farashin danyen man fetur ya tashi sakamakon yakin.

A jiya Talata ne kuma aka samu sabanin ra’ayi game da dalilin da ya sa Amurka ta kaiwa Iran hari tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da kuma sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio.

Trump ya ce ya umurci Isra’ila da ta kaiwa Iran hari saboda yana da yakinin Iran na da niyyar fara kawo musu hari. A nasa bangaren shi kuma Marco Rubio ya sha banban, inda ya shaidawa manema labarai ranar Litinin cewa Amurka ta kaiwa Iran hari ne saboda fargabar da ake yi na cewa Iran zata mai da martani game da shirin kaiwa Tehran hari da Isra’ila ta yi.

Ya ce mun san Isra’ila zata kai hari, kuma mun san cewa za’a mai da martani ta kai hari kan sojin Amurka, mun san idan bamu far musu ba zasu yi mana barna me yawa.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Pakistan Da Afghanistan Sunyi Arrangama
Next Post: Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
Ukraine Takai Hari Wajen Kera Makami Mai Linzami A Rasha Labarai
Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo
  • Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
  • Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki Najeriya
  • Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
  • Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.