An gurfanar da dan tsohon shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe a wata kotu a kasar Afrika ta Kudu ranar Litinin inda ake tuhumar sa da yunkurin aikata kisan kai, bayan da aka harbe, tare da raunata wani me kula da furanni a makon daya gabata a wani gida a birnin Johannersburg, inda dan Mugaben ke zama.
Ana zargin Bellarmine Chatunga Mugabe tare da wani da yunkurin kashe mutumin, wanda yanzu ke kwance a Gadon asibiti.
Bellarmine Chatunga Mugabe, wanda shine auta ga tsohon shugaban na Zimbabawe zai ci gaba da zama a tsare, har sai zuwa kotu na gaba, kamar yadda alkali ya zartar.
An dage karar har sai zuwa ranar 3 ga Watan Maris mai zuwa.


