Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya
Published: December 25, 2025 at 5:39 PM | By: Bala Hassan

Ba a maye gurbin Gbajabiamila da Muri-Okunola ba — Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya ta musanta wani labari na ƙarya da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sauya Shugaban Ma’aikatan Fadarsa (Chief of Staff), Hon. Femi Gbajabiamila, da Babban Sakataren Sirrinsa (Principal Private Secretary), Hakeem Muri-Okunola.

A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar a ranar Alhamis, ta bayyana cewa babu wata gaskiya ko kaɗan a cikin wannan ikirari, tare da kira ga ’yan Najeriya da su yi watsi da labarin gaba ɗaya.

Sanarwar ta jaddada cewa Hon. Femi Gbajabiamila na nan daram a matsayin Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, yayin da Hakeem Muri-Okunola shi ma ke ci gaba da gudanar da aikinsa a matsayin Babban Sakataren Sirri. Ta ce babu wani sauyi da aka yi a wadannan mukamai.

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa labarin da ke yawo ƙirƙirarre ne daga wasu masu yaɗa labaran ƙarya da nufinsu shi ne tayar da zaune tsaye da rashin jituwa a cikin gwamnati.

Haka kuma, ta sake jan hankalin kafafen yaɗa labarai da masu amfani da kafafen sada zumunta da su rika tantance sahihancin duk wani bayani kafin wallafawa ko yadawa.

Sanarwar ta samu sa hannun Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, a ranar 25 ga Disamba, 2025.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu
Next Post: Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar-Ta-Baci A Fannin Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
  • Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.