Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kwararru Sun Tabbatar Da Lafiyar Kangimi Dam Bayan Binciken Tsaro Afrika
  • Atiku: Zaben 2027 Zai Zamo Karo Na Karshe Da Zan Nemi Shugabancin Najeriya Afrika
  • Shugabannin Miyetti Allah Sun Nemi Sa Hannun Gwamnoni Wajen Sako Bello Bodejo Afrika
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi Afrika

Fiorentina Ta Yi Tayin Farko Ga Manchester United Kan Zirkzee
Published: August 28, 2026 at 1:01 PM | By: Bala Hassan

Fiorentina Ta Yi Tayin Farko Ga Manchester United Kan Joshua Zirkzee

Kungiyar Fiorentina ta gabatar da tayin farko a hukumance ga Manchester United domin daukar dan wasan gaban ta Joshua Zirkzee a matsayin aro, tare da zabin sayensa na dindindin.

Rahotannin yau sun tabbatar da cewa kungiyoyin biyu sun shiga tattaunawa kan yarjejeniyar.

An kuma ruwaito cewa Zirkzee ya amince da komawa Fiorentina, yayin da yanzu ake tattaunawa kan kudaden yarjejeniyar kafin United ta yanke hukunci kan tayin.

Wasu rahotanni sun ce tayin Fiorentina na iya kunshe da kudin aro kusan €5m, tare da zabin sayen dan wasan bayan kammala kakar wasa.

Zirkzee ya koma Manchester United daga Bologna a shekarar 2024, amma ya kasa samun daidaitaccen matsayi a kungiyar. Komawarsa Serie A na iya ba shi damar sake samun yawan buga wasa da kuma farfado da kwarewarsa.

Yanzu dai abin da ake jira shi ne amsar Manchester United kan tayin Fiorentina.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Kwararru Sun Tabbatar Da Lafiyar Kangimi Dam Bayan Binciken Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Arsenal Ta Doke Manchester City 3-0, Ta Ɗauki Kofin Community Shield Wasanni
Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
AFCON ChelIe, Ya Fidda Sunayen ‘Yan Wasan Super Eagles Na Karshe. Wasanni
Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fiorentina Ta Yi Tayin Farko Ga Manchester United Kan Zirkzee
  • Kwararru Sun Tabbatar Da Lafiyar Kangimi Dam Bayan Binciken Tsaro
  • Za a Fara Kakar Gasar Firimiya Ta Najeriya, NPFL, 2026/27 Yau Juma’a, 28 Ga Watan Agusta
  • Atiku: Zaben 2027 Zai Zamo Karo Na Karshe Da Zan Nemi Shugabancin Najeriya
  • Shugabannin Miyetti Allah Sun Nemi Sa Hannun Gwamnoni Wajen Sako Bello Bodejo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
  • Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.